Manyan Labarai A Yau
Mutane 2 sun rasu, wasu 13 sun nutse a ruwa yayin da jirgin fasinja ya yi taho mu gama da jirgin kamun kifi a jihar Bayelsa ranar Talata da ta gabata.
Dan takarar shugaban kasa na LP a zaben 2023, Peter Obi, ya caccaki kamun ludayin mulkin Shugaba Bola Tinubu. Ya ce da shi ne da ya sauya Najwriya cikin shekara 2.
Shugaba Bola Ahmed Tinubu zai tashi zuwa birnin Paris, na kasar Faransa, a yau Laraba domin wata gajeriyar ziyarar aiki, kamar yadda fadar shugaban kasa ta sanar.
Gwamnan jihar Ebonyi, Francis Nwifiuru bai ji dadin yadda wasu kwamishinonins ada 'yan kwangila suka kawo cikas ga wasu ayyuka a jihar ba. Ya umarci su zage damtse.
Gwamnan jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, ya nuna damuwa kan kwacewa mutsne filayensu. Ya gargadi masu rike da sarautun gargajiya da su guji yin hakan.
An shiga alhini a Kano bayan rasuwar Galadiman Kano, Alhaji Abbas Sanusi, mai shekaru 92. Kanawa sun aika sakonnin ta'aziyya ga iyalan marigayi Galadiman Kano.
Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya sanar da yin sauyin shugabanci a kamfanin NNPCL. 'Yan Najeriya sun yi martani kan cire Mele Kyari daga mukaminsa.
Jami'an hukumar tsaro ta DSS sun samu nasarar cafke wasu daga cikin manyan wadanda ake zargi da yi wa mafarauta 'yan Arewa kisan gilla a jihar Edo.
Wata ƙungiyar musulmi (TMC) ta buƙaci al'umma su kwantar da hankulansu, ka da a ɗauki fansa kan kisan gillar da aka yi wa ƴan Arewa mafarauta a Edo.
Manyan Labarai A Yau
Samu kari