Babbar Magana: INEC Ta Dauko Batun Takardun Karatun Shugaba Tinubu

Babbar Magana: INEC Ta Dauko Batun Takardun Karatun Shugaba Tinubu

  • Hukumar INEC ta bayyana dalilin da ya sa ba a wallafa takardun firamare da sakandaren Shugaba Bola Tinubu cikin takardun da aka fitar ba
  • Wani babban jami’in hukumar ya ce INEC kawao ta wallafa takardun da ’yan takarar suka gabatar mata
  • Kalu Agu ya shigar da ƙorafi kan Tinubu, yana zargin ya gabatar da takardun shaidar karatu na bogi ga INEC

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

​​​​​​​​​​​​​​Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi

Jihar Osun - Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) ta bayyana dalilin da ya sa takardun shaidar makarantar firamare da sakandare na Shugaba Bola Tinubu ba su cikin takardun da aka wallafa na ’yan takarar shugaban ƙasa a zaɓen 2027

Wani babban jami’in hukumar da ya nemi a sakaya sunansa ya ce INEC ta wallafa ne kawai takardun da ’yan takarar suka gabatar mata, kuma ba ta da ikon tambaya ko sauya takardun shaidar da aka miƙa mata.

Kara karanta wannan

Ana kaɗa ƙuri'a a Osun, ƴan sanda sun faɗi tanadinsu kan zaben Bauchi

Tinubu bai mika wasu takardu ba
Shugaban kasar Najeriya, Bola Ahmed Tinubu Hoto: @aonanuga1956
Source: Twitter

Jami’in ya shaida wa jaridar The Punch cewa manufar wallafa takardun ita ce bai wa jama’a damar duba su tare da gabatar da ƙorafi idan suna da wata matsala da suka lura da ita.

“Abin da aka gabatar wa hukumar kawai muka wallafa. Ba mu da ikon tambayar waɗannan takardun. Abin da muka yi shi ne wallafa su domin duk wanda yake da ƙorafi ya iya bayyana matsalarsa kan abin da muka wallafa,” in ji jami’in

Abin da INEC ta ce

Wannan bayani na INEC ya biyo bayan tambayoyin da wasu ’yan Najeriya suka yi bayan hukumar ta wallafa takardun shaidar ’yan takarar shugaban ƙasa na zaɓen 2027.

An lura cewa takardun shaidar makarantar firamare da sakandare na ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar All Progressives Congress (APC), Bola Tinubu, ba su cikin takardun da hukumar ta bayyana ga jama’a.

A cewar jami’in, INEC ba ta da hurumin yin tambayoyi ko sauya takardun da ɗan takara ya gabatar mata, sai dai ta wallafa su domin jama’a su duba tare da ɗaukar matakin da ya dace idan akwai abin da suke adawa da shi.

Kara karanta wannan

An sanya sunayen 'yan takarar gwamna na ADC su 28 a shafin INEC

Kalu Agu ya shigar da korafi

Hakan na zuwa ne bayan, Kalu Agu, wani lauya kuma jigon ADC, ya shigar da ƙorafi kan Tinubu ga Hukumar Tarayyar Turai da ke Brussels, Belgium

Agu ya zargi Shugaban ƙasar da gabatar da takardun shaidar karatu na bogi ga INEC a matsayin wani ɓangare na sharuddan kundin tsarin mulki da ake buƙata domin takarar shugaban ƙasa a 2027

Sai dai bayanin da INEC ta yi ya nuna cewa takardun da hukumar ta wallafa sun dogara ne kan waɗanda ’yan takarar suka gabatar mata, yayin da duk wani ƙorafi kan bayanan da ke cikin takardun ko sahihancinsu za a iya gabatar da shi ta hanyoyin da doka ta tanada.

Shugaba Tinubu ya mika takardu ga INEC
Shugaba Bola Ahmed Tinubu na Najeriya Hoto: Bayo Onanuga
Source: Twitter

Adeleke ya yabawa Tinubu

A wani labarin kuma, kun ji cewa gwamnan jihar Osun, Ademola Adeleke, ya yabawa Shugaba Bola Tinubu bayan sake zabensa a matsayin gwamnan jihar a zaben da aka gudanar ranar 15 ga Agustan 2026.

Gwamna Adeleke ya tabbatar da cewa Shugaba Tinubu ya kira shi domin taya shi murnar nasarar da ya samu a zaben.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal (Hausa Editor) Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng