Sarki Ya Shaka Kunya da Ya Roƙi Kujerar da Gwamna Ya Zauna Kanta a Wurin Ibada

Sarki Ya Shaka Kunya da Ya Roƙi Kujerar da Gwamna Ya Zauna Kanta a Wurin Ibada

  • Sarkin Iyin-Ekiti ya nemi a ba shi kujerar da Gwamna Biodun Oyebanji ya zauna a lokacin ibada domin kai ta fada
  • Fadar Oluyin ta ce an bukaci kujerar ne domin kula da ita da kuma gudanar da wasu bukukuwan gargajiya
  • Cocin Anglican ta ki mika kujerar, tana mai cewa an sake fasalinta kuma an hade ta da kayan bagadin cocin

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Ekiti - Cocin Anglican ta Babamuboni da ke Iyin-Ekiti ta ki amincewa da bukatar wani Sarki a jihar.

Sarkin Iyin-Ekiti, Adeniyi Adeola Ajakaiye ya buƙaci a mika masa wata kujera da Gwamna Biodun Oyebanji ya zauna kanta.

Sarki ya bukaci kujerar da gwamna ya zauna a coci
Gwamnan Ekiti, Biodun Oyebanji yayin ziyara a coci. Hoto: Biodun Oyebanji.
Source: Facebook

Sarkin ya bukaci a kai kujerar da Gwamnan Ekiti, Biodun Oyebanji, ya yi amfani da ita a wani taro na musamman zuwa fadarsa, cewar TheCable.

Kara karanta wannan

Dalilai 5 da suka sa Adeleke ya tumurmusa APC a zaben Osun

A ranar 31 ga Mayu, 2026, Oyebanji ya halarci bikin cikar Omolade Foluso Bamidele, kanin Opeyemi Bamidele, shugaban majalisar dattawa, shekaru 60.

An gudanar da bikin ne a cocin Babamuboni Memorial Anglican da ke Iyin-Ekiti, kwanaki kadan kafin zaben gwamnan Ekiti na 2026.

Bayan kammala ibadar godiyar, Oluyin na Iyin-Ekiti ya bukaci a ba shi kujerar da gwamnan ya zauna a kanta.

A wata wasika mai kwanan wata 17 ga Yuni, 2026, wadda aka aika wa limamin cocin, fadar Oluyin ta bukaci a kai kujerar fada.

Fadar ta ce za a ajiye kujerar ne domin “kula da ita a matsayin ta sarauta da kuma gudanar da bukukuwan gargajiya da suka dace”.

Wasikar, wadda Elejide Omobulejo, sakataren majalisar Oluyin, ya sanya wa hannu, ta ce majalisar ta yanke shawarar neman kujerar bayan tuntuba.

Ta ce:

“Bayan tuntuba da tattaunawa, majalisar Oluyin-in-Council ta yanke shawarar cewa a gaggauta kai kujerar da lamarin ya shafa zuwa fadar Oluyin.”

Majalisar ta ce kujerar za ta kasance karkashin kulawar sarauta, tare da gudanar da bukukuwan gargajiya da suka dace.

Kara karanta wannan

Zaben 2027: Gwamnan Kebbi Ya ajiye mataimakinsa, ya dauko sabon abokin takara

Ta kuma bukaci a sanya sabuwar kujera da za a samar a karkashin tsauraran matakan tsaro domin kauce wa sake faruwar irin wannan lamari.

Fadar ta bayyana cewa lamarin ya sake tabbatar da mutunta juna da kyakkyawar alakar da ta dade tana tsakanin fadar da cocin.

Martanin da Cocin ya yi ga bukatar

A wata wasika mai kwanan wata 18 ga Yuni, 2026, cocin ta sanar da fadar cewa ba za ta iya “mika, canja ko cire” dukiyar cocin ba.

Cocin ta ce ba za ta iya mika dukiyar cocin domin wasu ayyukan waje ba, sai an bi hanyoyin da hukumomin addinin Anglican suka tanada.

Ta kuma bayyana cewa kujerar da ake magana a kai ba ta wanzu cikin irin yanayin da take a lokacin ibadar godiyar.

Cocin ta ce ana gudanar da gyare-gyare da sake fasalin ginin, lamarin da ya sa aka cire kujeru da sauran kayan daki daga wuraren da suke.

Wasikar ta ce: “Saboda haka, cocin ba ta da damar mika, canja ko cire dukiyar cocin domin wasu ayyuka na waje.”

Kara karanta wannan

EFCC ta kai wani mutum kotu kan zargin baba kere da N56m na kudin aikin hajji

Ta kara da cewa a matsayinsu na masu kula da dukiyar cocin, wajibi ne su kiyaye ta bisa koyarwa, dokoki da tsarin gudanarwar cocin.

Cocin Anglican ta ce tsarin gudanarwarta yana karkashin shugabancin bishops da kuma tsarin majalisar synod, don haka ba jami’an cocin yankin kadai ke yanke irin wannan hukunci ba.

Ta ce duk shawarar da ta shafi dukiyar cocin, kayan ibada da gudanar da harkokin cocin tana bukatar bin ka’idojin tsarin addinin Anglican.

Cocin ta ce amincewa da bukatar fadar zai haifar da wasu batutuwan gudanarwa da suka wuce ikon da aka bai wa cocin yankin.

Ta kuma jaddada cewa kujerar da fadar ta nema ba ta wanzu a matsayin kujera mai zaman kanta da za a iya cirewa.

Cocin ta bayyana cewa yayin gyaran ginin, an cire tsofaffin kujeru da sauran kayan daki daga tsarin da suke a baya.

Ta ce an raba wasu daga cikinsu ga wasu majami’u domin ci gaba da amfani da su, yayin da ake girke sababbin kujeru.

Cocin ta ce kujerar da ake magana a kanta an sake ginawa, an rage girmanta sannan aka hade ta da kayan bagadin cocin.

Kara karanta wannan

'Yan Najeriya na cikin alheri, an turo musu tallafin fiye da Naira biliyan 40 daga ƙasar waje

Saboda haka, cocin ta ce kujerar ba ta wanzu a matsayin wani abu mai zaman kansa da za a iya cirewa a kai wani wuri.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.