Labaran garkuwa da mutane
'Yan bindiga a wasu hare-hare sun sake sheke mutane akalla 5 a wasu sassan jihar Kaduna. Samuel Aruwan, kwamishinan tsaro da harkokin cikin gida ne ya tabbatar.
Wasu yan bindiga da ba'asan ko su waye ba sun yi awon gaba da wani yaro ɗan shekara 13 a jihar Osun, sun nemi iyalan yaron su biya miliyan N50 kuɗin fansa.
Rundunar 'yan sanda a jihar Kaduna ta ceto wasu mutane 15 dda aka sace a hanyar Birnin Gwari na jihar ta Kaduna. Sun kuma kwato shanu sama da 30 a aikin cetnon.
Wani sojan Najeriya ya kubuta daga hannun 'yan bindiga bayan shafe kwanaki a hannunsu. Ya samu nasarar hallaka biyu daga cikinsu ya kuma tsere daga sansaninsu.
Gwamna El-Rufai ya bayyana cewa, dukkan 'yan bindiga ko a ina suke a Najeriya ya kamata a kamesu a ji dasu. Ya ce, babu wanda ya cancanci rayuwa a cikinsu.
Wasu 'yan bindiga sun yi awon gaba da wani shugaban ƙaramar hukuma a jihar Rivers mai suna, Philemon Kingoli, sai dai har yanzun basu tuntubi yan uwansa ba.
Rundunar 'yan sanda a jihar Ogun, ta tabbatar da cewa waɗansu 'yan China guda biyu da yan bindiga suka sace a satin da ya gabata sun kuɓuta daga hannun su.
Rundunar yan sandan ƙasar nan reshen jihar Osun sun tabbatar da sace wasu yan ƙasar Chine dake zama a Najeriya guda biyu a wajen haƙar ma'adanai dake jihar.
Gwamnan jihar Kaduna ya bayyana dalilan da yasa 'yan bindiga suka addabi jihar ta Kaduna da kai hari. Yace saboda jihar ba za ta bada kudin fansa bane ko kwabo.
Labaran garkuwa da mutane
Samu kari