'Yan bindiga sun sake kai farmaki yankin Kaduna, sun sheke mutane biyar

'Yan bindiga sun sake kai farmaki yankin Kaduna, sun sheke mutane biyar

- Rahotannin tsaro daga jihar Kaduna sun tabbatar da mutuwar wasu mutane biyar a wasu sassan jihar

- An bayyana cewa, mutanen sun mutu ne a wasu hare-hare daban-daban na 'yan bindiga a yankin

- Kwamishinan Tsaro da Harkokin Cikin Gida Samuel Aruwan ne ya bayyana faruwar lamarin

Kwamishinan Tsaro da Harkokin Cikin Gida, Mista Samuel Aruwan ya tabbatar da cewa an kashe mutane biyar a kananan hukumomin Zango-Kataf da Giwa a ranar Litinin, jaridar Punch ta ruwaito.

Kwamishinan a baya cikin wata sanarwa ya ce mutane biyu; uba da da, Joshua Dauda da dansa mai shekaru bakwai, Philip, a kauyen Wawan an kai musu hari a karamar hukumar Zangon-Kataf.

Duk da haka, yayin da yake sabunta rahoton, kwamishinan ya ce karin gawarwakin biyu jami'an tsaro sun gano su.

KU KARANTA: Zulum da Sanatocin Borno sun ziyarci CDS da COAS kan batun Boko Haram

'Yan bindiga sun sake kai farmaki yankin Kaduna, sun sheke mutane biyar
'Yan bindiga sun sake kai farmaki yankin Kaduna, sun sheke mutane biyar Hoto: bbc.com
Asali: UGC

"Bugu da kari ga bayanin farko kan harin da aka kai a kauyen Wawan Rafin da ke karamar hukumar Zangon Kataf, hukumomin tsaro sun bayar da rahoton cewa an gano gawarwakin wasu karin mutane biyu a yankin," in ji shi.

Aruwan ya bayyana wadanda lamarin ya rutsa da su da Francis Ayuba da wani karamin yaro, Florence Dennis, ya kara da cewa:

"Wannan ya kawo adadin wadanda suka mutu daga harin zuwa hudu, wadanda aka lissafa kamar haka: Joshua Dauda, ​​Philip Dauda, ​​Francis Ayuba da Florence Dennis."

Har ila yau, a wani labarin, kwamishinan ya ce ‘yan bindigar sun afka wa wata gonar rake a wajen Iyatawa a karamar hukumar Giwa suka harbe wani Isah Haruna, mazaunin yankin.

A cewarsa, hukumomin tsaro sun bayar da rahoton cewa an fatattaki gungun 'yan bindiga a Rugan Bello, wani matsuguni da ke kan hanyar Kajuru-Buda a karamar hukumar Kajuru ta jihar.

KU KARANTA: Kuri'un talakawa ya kamata su tattance zabe ba kotu ba, in ji Jonathan

A wani labarin, Wasu rahotanni sun ce wasu gungun mutane sun kashe tare da kone wasu mutane uku da ake zargin ‘yan bindiga ne a garin Magamar Jibia da ke karamar hukumar Jibia a Katsina.

Lamarin ya faru ne lokacin da wasu ‘yan bindiga suka mamaye garin da misalin karfe 11:25 na daren ranar Lahadi.

Wani mazaunin garin ya shaida wa jaridar Daily Trust cewa ’yan bindigan sun kutsa kai cikin gidan wani mutum da ba a bayyana sunansa ba, wanda ya yi kukan kura mazauna garin kuma suka tattara suka yi wa 'yan bindigan kawanya.

Asali: Legit.ng

Online view pixel