Gwamna Ya Gaji, Ya Fadi Inda Zai Rataye Masu Garkuwa da Mutane a cikin Birni
- Gwamnan Edo Monday Okpebholo ya nuna damuwa game da karuwar laifuffukan asu garkuwa da mutane a jihar
- Ya ce za a kafa kotu ta musamman domin gaggauta shari’a da aiwatar da hukunci a fili don tsoratar da masu aikata laifi
- Okpebholo ya ce gwamnati tana aiki tare da ‘yan sanda, soja da DSS domin kawo ƙarshen ta’addanci da tabbatar da tsaro a Edo
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.
Benin-City, Edo - Gwamnan Edo, Monday Okpebholo, ya yi barazana ga masu da garkuwa da mutane a jihar.
Gwamna ya bayyana cewa za a aiwatar da hukuncin kisa a fili kan waɗanda aka samu da laifin garkuwa da mutane da ‘yan daba bayan an yanke musu hukunci a jihar.

Source: Twitter
Gwamnan ya bayyana hakan ne yayin da yake ganawa da ‘yan jarida a lokacin da aka gabatar da wasu da ake zargi da garkuwa da mutane da rundunar ‘yan sanda ta kama, cewar TheCable.

Kara karanta wannan
Dubu ta cika: An rushe katafaren gidan kasurgumin mai garkuwa da mutane da aka cafke a Edo
Gwamna zai kafa kotun masu garkuwa da mutane
Ya ce gwamnatinsa za ta kafa kotu ta musamman domin shari’ar masu laifi cikin gaggawa, sannan kuma a aiwatar da hukuncin kisa a fili domin zama izina ga wasu.
Ya ƙara da cewa ya kamata jama’a su guji shiga harkar daba da garkuwa da mutane domin hakan ba zai kai su ko’ina ba.
Ya ce:
“Ba wasa mu ke ba. Muna aiki dare da rana domin tabbatar da wannan ƙasa ta kasance lafiya.”
“Yanzu za mu kafa kotu ta musamman domin shari’ar masu garkuwa da mutane da ‘yan daba. A cikin makonni biyu zuwa uku za mu kammala. Zan kuma rattaba hannu a kai.”
“Game da hukuncin kisa da rataya, zan kai ku filin shataletale na 'Ring Road' domin duk mutanen Edo su gani. Ba zan yi nadama ba.”

Source: Twitter
Umarnin da Gwamnan Edo ya ba yan sanda
Gwamnan ya kuma bayyana wani lamarin garkuwa da mutane da ya faru a kasuwa a babban birnin jihar a karshe makon da ya gabata.
Ya ce nan take ya tuntubi kwamishinan ‘yan sandan jihar tare da umartar a kama duk masu hannu a lamarin, cewar Punch.
A cewarsa, kwamishinan ‘yan sandan da ke Abuja a lokacin ya dawo Benin City nan take, inda ya jagoranci aikin da ya kai ga kama wasu daga cikin wadanda ake zargi.
Daga baya jami’an tsaro sun bi sawun masu laifin zuwa maboyarsu, inda aka kashe ɗaya a musayar wuta, aka kama ɗaya, yayin da wasu biyu suka tsere.
Gwamnan ya yaba wa ‘yan sanda, sojoji da DSS bisa ƙoƙarinsu wajen yaki da rashin tsaro a jihar.
'Yan sanda sun bindige yan bindiga
Mun ba ku labarin cewa rundunar ‘yan sandan Najeriya a ta kashe wani da ake zargi mai garkuwa da mutane ne tare da kama wani da ake zato yana satar mutane a Edo.
Rahoto ya nuna cewa an ƙwato mota, bindiga, harsasai biyu da tsabar kudi Naira miliyan 2.25 da kuma babur daga wajen wana aka kama.
Biyo bayan lamarin, Gwamna Monday Okpebholo na jihar Edo ya bayyana shirin kafa kotu ta musamman domin shari'ar masu garkuwa da mutane.
Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.
Asali: Legit.ng
