An Ga Tsohon Dan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa, Okowa a Ofishin Hukumar EFCC

An Ga Tsohon Dan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa, Okowa a Ofishin Hukumar EFCC

  • Tsohon gwamnan Delta, Sanata Ifeanyi Okowa, ya kai ziyara ofishin EFCC da ke Legas yayin da ake ci gaba da bincike kan zargin karkatar da Naira tiriliyan 1.3
  • Rahotanni sun ce tsohon dan takarar mataimakin shugaban kasar ya je ne domin neman a maido masa fasfo dinsa na tafiya kasashen waje
  • EFCC na zarginsa da karkatar da kudaden 13% na rabon mai da kuma sayen kadarori da kudaden gwamnati

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Lagos, Nigeria - Tsohon gwamnan jihar Delta kuma dan takarar mataimakin shugaban kasa na PDP a zaben 2023, Sanata Ifeanyi Okowa, ya kai ziyara ofishin Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa (EFCC) da ke Ikoyi a Legas.

Wannan ziyara da Okowa ya kai na zuwa ne yayin da hukumar EFCC ke ci gaba da bincike kan zargin karkatar da Naira tiriliyan 1.3 na kudaden gwamnatin Delta a lokacin mulkinsa.

Kara karanta wannan

Rarara ya zargi Kwankwaso da jefa Najeriya cikin halin kunci, ya kawo dalili

Okowa.
Tsohon gwamnan jihar Delta, Ifeanyi Okowa a taron addu'a a coci Hoto: Ifeanyi Okowa
Source: Facebook

Majiyoyi daga hukumar sun shaida wa Leadership cewa ziyarar Okowa na da nasaba da binciken kudaden kaso 13 na jihohi masu arzikin fetur wanda Delta ta karba tsakanin 2015 zuwa 2023.

Hukumar EFCC ta taba kama shi a 2024

A ranar 4 ga Nuwamban 2024 ne EFCC ta kama Okowa tare da tsare shi domin yi masa tambayoyi a ofishinta na shiyyar Fatakwal kan wannan batu.

Rahotanni sun nuna cewa babban dalilin ziyararsa ta baya-bayan nan shi ne neman a mayar masa da fasfo dinsa na kasa da kasa.

An ce ya shaida wa masu bincike cewa yana bukatar tafiya kasashen waje domin neman kulawar lafiya cikin gaggawa.

Sai dai har zuwa lokacin hada wannan rahoto ba a tabbatar ko EFCC ta amince da bukatarsa ko ta mayar masa da fasfon ba.

Ana zarginsa da karkatar da kudade

A watan Nuwamban 2024, EFCC ta bayyana cewa tana binciken Okowa kan zargin karkatar da Naira tiriliyan 1.3 a lokacin da ya yi shekaru takwas yana gwamnan jihar Delta.

Kara karanta wannan

Yau ake gudanar da zabe a Kano, Ekiti da wasu jihohin Najeriya

Haka kuma ana zarginsa da amfani da kudaden gwamnati wajen sayen kadarori a Asaba, babban birnin jihar Delta, da kuma Abuja.

Okowa ya musanta aikata laifi

Da yake magana bayan kama shi a wancan lokaci, Okowa ya ce an yi amfani da kudaden jihar yadda ya kamata a lokacin mulkinsa.

Ya kuma bayyana cewa bai damu da binciken da ake yi masa ba, yana mai cewa ba ya tsoron a bincike shi.

“Duk abin da ke faruwa, ban damu ba. Na fada a baya cewa ban tsoron a bincike ni,” in ji Okowa.
EFCC.
Babbar hedkwatar hukumar EFCC ta kasa da ke Abuja Hoto: @officiEFCC
Source: Twitter

A watan Afrilun 2025, Okowa ya sauya sheka zuwa jam’iyyar APC tare da magajinsa, Gwamna Sheriff Oborevwori, da wasu manyan yan siyasa a jihar Delta.

EFCC ta tsare shugaban hukumar ECN

A wani labarin, kun ji cewa jami'an hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta EFCC, sun tsare shugaban hukumar makamashi ta Najeriya (ECN), Mustapha Abdullahi.

Majiyoyi daga EFCC sun bayyana cewa zargin da ake yi wa shugaban na hukumar makamashi ta Najeriya ya shafi kudade wanda adadinsu ya kai N500bn.

An naɗa Mustapha Abdullahi ne a matsayin shugaban ECN bayan ya shafe shekaru fiye da 10 yana aiki a hukumar NUPRC ta Najeriya.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262