Labaran garkuwa da mutane
Rahoto ya bayyana cewa, wasu daga cikin daliban makarantar Baptist ta Kaduna da aka sace a yau sun samu sun kubuta daga hannun 'yan bindigan da suka sace su.
A karo na biyu, wasu mutane ɗauke da makamai sun kutsa cikin gidan shugaban NLC reshen Taraba, inda suka yi awon gaba da shi zuwa wani wuri da ba'a sani ba.
Jihar Kaduna na ɗaya daga cikin jihohin arewa maso yammacin Najeriya dake fama da yawan harin yan bindiga a makarantun ɗalibai, an sake sace wasu yau Litinin.
Wasu 'yan bindiga sun kai hari wani yankin jihar Katsina. Sun hallaka wani mutum tare da wawashe shagon cajin wayoyi. Sun yi arangama da 'yan sanda a yankin.
Jihar Akwa Ibom na ɗaya daga cikin jihohin yankin kudu dake fama da harin yan bindiga a kan jami'an tsaro, wasu yan ta'adda sun jikkata jami'ai uku a jihar.
Rundunar 'yan sanda a jihar Kaduna sun tabbatar da ceto wani jariri dan wata 10 daga hannun wata 'yar aikin da ta sace shi zuwa wani wuri. Ana kan bincike.
Rundunar 'yan sanda ta cafke wasu bata-gari da suka sace wani mutum, kuma suka hallaka shi bayan karbar kudin fansa. An gano abubuwa da dama daga hannunsu.
Bayan wasu yan bindiga da ba'a san ko suwaye ba sun hallaka ɗan majalisa mai wakilatar Shinkafi a majalisar dokokin Zamfara, Gwamna Matawalle ya nuna alhininsa.
Rahoto ya bayyana cewa, an yi awon gaba da matar Sunday Igboho mai fafutukar kafa kasar Yarbawa kwanaki kadan bayan kame shugaban kungiyar IPOB Nnamdi Kanu.
Labaran garkuwa da mutane
Samu kari