Labaran kasashen waje
Jamhuriyar musulunci ta Iran ta sake kai farmaki yankunan Isra'ila ranar Juma'a, hukumar agaji ta tabbatar da cewa akalla mutane 17 ne suka raunata.
Tinubu zai kai ziyara ta mako guda zuwa Saint Lucia daga 28 ga Yuni, inda zai shafe kwanaki biyu yana ziyarar aiki, sannan sauran kwanaki kuwa ya hutu a cikin kasar.
Ma'aokatar lafiya ta kasar Iran ta tabbatar da cewa harin Isra'ila ya taɓa wani babban asibiti a birnin Tehran, an lalata motocin ɗaukar marasa lafiya.
Isra'ilawa sama da 8,000 sun rasa matsugunansu sakamakon hare-haren da Iran ke ci gaba da kai kan ƙasarsu, wannan rahoto na zuwa ne mako 1da fara rikici.
Bayan hare-haren da Isra’ila ta kai cikin Iran, kawayenta sun yi gum, sai Rasha ce kaɗai ta tsaya da ita, yayin da CRINK ke kiran zaman sulhu a yankin.
Farmakin makami mai linzami daga Iran ya jawo rufe tashar jirgin ƙasa ta birnin Beersheba a ƙasar Isra'ila, harin ya taɓa cibiyar fasaha da sansanin soji.
Iran ta kai farmaki kan babbar cibiyar kimiyya ta Weizmann a Isra’ila, ta lalata dakunan gwaje-gwaje, a matsayin ramuwar gayya kan kashe masananta.
Rahotanni sun nuna cewa makamai 2 da ake kyautata zaton Iran ce ta harbo su sun faɗa wasu yankuna a ƙasar Jordan, sun raunata yarinya tare da ɓarnata dukiya.
Isra’ila ta tura jiragen yaki, inda suka lalata cibiyar Arak da take zargin Iran na amfani da ita don hada nukiya. Iran ta ce harin bai yi wani barna a cibiyar ba.
Labaran kasashen waje
Samu kari