Izala Ta Shirya Babban Taro na Tarihi a Abuja, an Gayyaci Manyan Baki

Izala Ta Shirya Babban Taro na Tarihi a Abuja, an Gayyaci Manyan Baki

  • Kungiyar Jama’atu Izalatil Bidiah wa Iqamatis Sunnah (JIBWIS Nigeria) za ta shirya babban taro a birnin tarayya Abuja
  • Izala za ta shirya taron ne tare da hadin gwiwar Muslim World League kan tsaro na kasa, inda aka gayyaci manya-manyan mutane
  • Daga cikin mutanen da ake sa ran za su halarci taron har da shugaban kasar Najeriya, mai girma Bola Ahmed Tinubu

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

​​​​​​​​​​​​​​Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi

FCT, Abuja -Najeriya za ta karɓi bakuncin wani gagarumin taron duniya yayin da Jama’atu Izalatil Bidiah wa Iqamatis Sunnah (JIBWIS Nigeria), tare da haɗin gwiwar Muslim World League, suka shirya babban taro.

Kungiyar JIBWIS da hadin gwiwar Muslim World League sun shirya taron Kasa da Kasa kan Tsaro na Ƙasa domin dorewar ci gaban zamantakewa da tattalin arziki.

JIBWIS ta shirya babban taro
Shugaban kungiyar Izala, Sheikh Bala Lau Hoto: JIBWIS Nigeria
Source: Facebook

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da Legit Hausa ta samu a ranar Alhamis, 6 ga watan Yulin 2026.

Kara karanta wannan

Bayan sako malamai a gaba, Ibrahim Dahiru Bauchi ya je wajen Tinubu a Abuja

Za a gudanar da muhimmin taron ne a dakin taro na International Conference Centre, Abuja, daga ranar 11 zuwa 13 ga Agusta 2026.

Wannan babban taron kasa da kasa zai haɗa manyan malamai na addinin Musulunci, shugabannin tunani na duniya, kwararrun masu tsara manufofi, masu kare bambance‑bambance, da manyan jami’an gwamnati daga cikin gida da waje.

A wani lokaci da ƙasashe ke fuskantar ƙalubalen tsaro, rikice‑rikicen siyasa, da damuwar addini da kabilanci, wannan taro zai zama fitilar fata, dandamali da aka tsara domin ƙarfafa tattaunawa, inganta haɗin gwiwa, da shimfiɗa hanya mai ɗorewa zuwa zaman lafiya, kwanciyar hankali, da ci gaba.

Bude taron zai samu jagorancin Mai Girma Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, GCFR, alamar muhimmancinsa ga ƙasa da kuma tasirinsa a duniya.

Manyan baƙi, ciki har da shugabannin bangaren shari’a, kwararrun tsaro, da jakadu daga ƙasashen duniya, za su halarta a matsayin baƙi na musamman da masu gabatar da muhimman jawabai.

Kara karanta wannan

Babbar magana: Ma'aikata sun huro sabuwar wuta ga Shugaba Tinubu

Wannan muhimmin haɗin gwiwa tsakanin JIBWIS Nigeria da Muslim World League na nuna kudurin su na inganta bambance‑bambance, zaman tare, haɗin kai tsakanin al’ummomi, da zaman lafiya mai ɗorewa.

Ya kuma ginu a kan manyan tattaunawa da aka yi a baya tsakanin jagororin Musulmi da Kiristoci a sassa daban daban na duniya a gefe guda da kuma mabambantan fahimtoci dake tsakanin al-ummah, tare da tabbatar da cewa addini da bambancin al’adu na da ƙarfi wajen gina haɗin kai, kwanciyar hankali, da cigaban al’umma.

Abubuwan da taron zai ƙunsa

  • Babban taro na manyan kwararru, mai mayar da hankali kan tsaro da ci gaban ƙasa a mahangar duniya
  • Zauren tattaunawa kan bambance‑bambance, domin inganta zaman lafiya da haɗin kai
  • Kwamitocin kwararru, kan yaki da tsattsauran ra’ayi da ƙarfafa juriyar al’umma
  • Taron teburin haɗin gwiwar duniya, domin inganta ci gaban zamantakewa da tattalin arziki mai ɗorewa
Izala ta shirya babban taro a birnin Abuja
Kungiyar Izala ta shirya babban taro kan tsaro a Abuja Hoto: JIBWIS Nigeria
Source: Facebook

Izala ta goyi bayan tazarcen Gwamna Abba

A wani labarin kuma, kun ji cew. kungiyar Jama'atu Izalatul Bidi'a Wa Iqamatis Sunnah (JIBWIS) reshen jihar Kano ta bayyana goyon bayanra ga tazarcen gwamna Abba Kabir Yusuf.

Kungiyar Izala ta bayyana cewa gwamnatin Abba ta karfafa jama'a, ta hanzarta kawo ci gaba, tare da daura jihar kan turbar samun ci gaba mai dorewa.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal (Hausa Editor) Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng