Yan bindiga
'Yan bindiga sun yi awon gaba da wani fasto da ke shugabantar wata coci a jihar Benue. Hatsabiban sun kuma hada har da wasu mambobin cocinsa yayin harin.
‘Yan bindiga sun kashe jami’an ‘yan sanda biyu tare da raunata wani a Rivers a wani shingen bincike, yayin da rundunar ta fara bincike don kamo maharan.
Dan Majalisar Wakilai na jam'iyyar APC daga jihar Plateau, Yusuf Gagdi, ya nuna alamar tambaya ga yan adawa kan matsalar rashin tsaron da ake fama da ita a Najeriya.
Bincike ya tabbatar da cewa babu wata hujja ingantacciya da ke tabbatar da cewa yaron da ya bayyana a wani hoto mai yaduwa shi ne ya sace Janar Rabe Abubakar.
Wani saƙo da ya yaɗu a kafafen sada zumunta ya yi ikirarin cewa an kama sarakunan Alabe da Babanla da matansu a Kwara bisa zargin garkuwa da mutane.
Shugaban cocin RCCG, Fasto Enoch Adeboye, ya bayyana cewa Ubangiji ya sanar masa yadda za a saki dalibai da malaman da 'yan bindiga suka sace a jihar Oyo.
'Yan bindiga dauke da makamai sun kai hare-hare a wasu garuruwan jihar Katsina. 'Yan bindigan sun hallaka wasu mutane tare da raunata wasu daban.
Shugaban cocin RCCG, Fasto Enoch Adeboye, ya kare shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu kan matsalar rashin tsaro. Ya ce ya yi bakin kokarinsa kan matsalar.
Karamin ministan harkokin wajen Najeriya, Ambasada Sola Enikanolaiye ya ce Najeriya na bukatar hadin kan kasashe kan yaki da rashin tsaro a fadin kasar nan.
Yan bindiga
Samu kari