Aikin Hajji
Hukumomi a kasar Saudiyya sun sauya suturar dakin Ka’aba a ranar Asabar, 10 ga watan Agustan 2019. Duk shekara ana cire rigar sannan a maye gurbinta da sabuwa a ranar tara ga watan Dhu Al-Hijjah, wanda ya yi daidai da ranar Asaba
Gwamna Bala Muhammad na jihar Bauchi, ya ce shi da wasu mukarrabansa da suke aikin hajjin suna zaune ne a gidan alhazai na gama-gari daga jihar, maimakon kasaitaccen masauki ko otal.
Hukumar da ke kula da jin dadin Mahajjatan Najeriya (NAHCON) ta bayyana cewa maniyyatan kasar shida ne suka rasu a kasar Saudiyya.
Legit.ng ta ruwaito wannan mutumi da ba’a bayyana sunansa ba ya ciccibi mahaifiyarsa dattijuwa a wuyarsa, inda ya dinga zagayen Ka’aba dakin Allah da ita, ma’ana dai ya gudanar da dawafi dauke da mahaifiyarsa a wuyarsa.
Babban malamin nan na kasar Saudiyya, Sheikh Abdul Rahman Al Sudais, ya bukaci mahajjata da su kiyayi ayyukan da ka iya siyasantar da aikin Hajjin.
A yayin da hadaya wato yanka dabba ta kasance wani rukuni cikin hukunce-hukunce na cikar ibadar aikin Hajji, wani al'amari ya taso a kanta tsakanin hukumar jin dadin Alhazai da maniyyatan jihar Kano.
A yayin da alhazai ke shirin fara gudanar da aikin Hajji a kasar Saudiyya, hukumar dake kula da alhazan Najeriya, NAHCON, ta bayyana wasu muhimman bayanai guda 8 game da aikin Hajji da dakin Allah, Ka’abah don amfanin mahajjata.
Gwamnatin kasar Saudiyya ta zabi harshen Hausa cikin harsunan Duniya da za’a dinga gabatar da tunatarwa a cikinsu a babban masallacin Madina, watau Masallacin Annabi Muhammadu tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi.
Bayan gwamnan Neja, wani Gwamnan Arewa ya tafi Hajji jiya. Gwamna Mala Buni ya tafi kasar Saudi ne da wasu mutanensa. Kafin nan kun ji labari cewa Ahmad Lawan da Femi Gbajabiamilla za su yi aikin hajjin bana.
Aikin Hajji
Samu kari