Juyin Mulki: Tijjaniya Ta Tayar da Maganar Zargin Sheikh Khalifa, Ta Ja Kunnensu
- Ƙungiyar Tijjaniyya ta shawarci miliyoyin mabiyanta yayin da ake ci gaba da tuhumar Sheikh Abdulkadir Sani Khalifa da ake yi
- Ta bukace su da su kauce wa furuci da zai iya dagula shari’ar Malamin da ake yi kan zargin hannu a juyin mulki
- An gurfanar da Sheikh Khalifa kan zargin shirin juyin mulki da ta’addanci, inda ya musanta tuhume-tuhume 13
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.
Kaduna - Ƙungiyar darikar Tijjaniyya ta yi magana game da ci gaba da tuhumar Sheikh Abdulkadir Sani Khalifa da ake yi kan hannu a juyin mulki.
Ƙungiyar ta bukaci mabiyan ta a Najeriya da su guji yin kalamai da za su iya kawo cikas ga shari’ar malamin da ke gudana a kotu.

Source: Facebook
A cikin wata sanarwa da Daily Trust ta samu, mataimakin shugaban majalisar shura ta Tijjaniyya, Sheikh Ibrahim Shehu Maihula, ya buƙaci mabiya su dage da addu’o’i domin samun nasarar malamin.
Musabbabin kama Sheikh Khalifa Zaria
An kama Sheikh Khalifa kusan watanni biyar da suka gabata, sannan aka gurfanar da shi a makon da ya wuce bisa zargin shirya juyin mulki a kan gwamnatin shugaba Bola Ahmed Tinubu.
Sai dai ya musanta dukkan tuhume-tuhume 13 da aka karanta masa a gaban babbar kotun tarayya da ke Abuja, inda aka ɗage shari’ar domin fara sauraron ƙarar.
Ƙungiyar Tijjaniyya ta bayyana cewa tana da yaƙinin kotu za ta wanke Sheikh Khalifa, kamar yadda a baya wata kotu ta bayar da umarnin a sake shi ba tare da wani sharaɗi ba.

Source: Facebook
An bayyana halayen Sheikh Khalifa Zariya
Sanarwar ta jaddada cewa Sheikh Khalifa fitaccen malamin addini ne wanda aka san shi da koyarwa mai zaman lafiya da kuma kira ga bin doka da oda a cikin al’umma.
Ta kuma bayyana yadda aka kama shi a hedikwatar bankin Ja’iz da ke Abuja bayan an dakatar da asusunsa, inda jami’an tsaro suka tafi da shi zuwa wani wuri da ba a sani ba.
Hakan ya jefa iyalansa da mabiya darikar cikin damuwa, musamman ganin cewa ya shafe watanni ba tare da ganawa da lauyoyinsa ko iyalansa ba har sai bayan an mayar da shi hannun DSS.
Daga baya, kotu ta yanke hukuncin cewa an take masa haƙƙoƙinsa, tare da umartar a sake shi da kuma cire takunkumin da aka sanya a asusun bankinsa.
Sai dai gwamnatin tarayya ta sake shigar da ƙara a kansa da wasu mutane biyar kan zargin ta’addanci, inda aka fara shari’ar a gaban kotu.
Ƙungiyar Tijjaniyyar ta buƙaci mabiya ta su kasance masu haƙuri da bin doka, tare da yin addu’o’i domin samun nasara a shari’ar da ke gudana, cewar Leadership.
Iyalan Sheikh Khalifa sun karyata labarin mutuwarsa
An ji cewa iyalan Sheikh Sani Abdulkadir Khalifa Zariya sun yi karin haske kan halin da yake ciki lokacin da ake ta yada jita-jitar rasuwarsa.
Ɗansa mai suna Ibrahim ya bayyana cewa an hana malamin ganawa da lauyoyi kuma hukumomi ba su ba su wani bayani ba kan binciken ba.
Iyalan sun buƙaci gwamnatin Najeriya ta gurfanar da shi a kotu idan akwai zargi tare da ba su damar ganin mahaifinsu.
Asali: Legit.ng

