‘Yan Siyasa 12 da Aka Taba Samu da Yi wa ‘Yan Adawa Barazana Lokacin Zabe
Abuja - A shekarar nan ana neman dawo da siyasar barazana, inda za a ji masu rike da mulki suna yin munanan kalamai.
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
M Malumfashi ya shafe shekaru 10 yana kawo labaran Hausa musamman na siyasa, addini, tarihi, wasanni da al’ada
Daga 'yan jam'iyya, gwamnoni, ‘yan majalisa zuwa shugabannin kananan hukumomi, an saba jin ‘yan siyasa suna neman tada hankali.
Rahoton nan ya bibiyi tarihi, ya tuno da ‘yan siyasar da aka taba ji sun bari giyar mulki ya ja su a kan aboka hamayyarsu daga 2015 zuwa yau.

Source: Getty Images
‘Yan siyasar da kalamansu suka nemi jawo rikici
1. Muhammad Gadaka
Kwanan nan aka ji shugaban APC na reshen Yobe, Muhammad Gadaka yana kira ga mata su bokarewa mazajensu wajen zaben jam’iyyarsu.
An rahoto cewa Alhaji Gadaka ya fada wa matan su nemi saki idan masu gidansu suka hana su zaben APC, yake cewa bayan nan shi zai aure su.
Da ya ji matin lamba da surutun jama’a, ‘dan siyasar ya yi maza ya nemi afuwar mutane.
2. Sainna Buba
A wani taron siyasa a Satumban 2026, Sainna Buba wanda ke rike da kujerar kwamishina a gwamnatin jihar Borno ya yi barazanar karya yatsun ‘yan adawa.
Leadership ta ce Kwamishinan na matasa da yaki da talauci ya janye kalaman da ya yi, ya ce bai kamata al’umma su yi amfani da zahirin maganganunsa ba.
3. Danjuma Shekwolo
Shi Danjuma Shekwolo ya dauko ta da zafi, domin ya yi barazanar za su kori duk wanda bai goyon bayan APC a karamar hukumar Kuje a birnin Abuja.
Da surutun jama’a ya yi, shugaban karamar hukumar ya yi kokarin wanke kan shi a cewar rahoton Arise. Lamarin ya kai 'yan sanda sun fara binciken su.
4. Francis Nwifuru
Mai girma gwamna Francis Nwifuru ya yi wa shugabannin kananan hukumomin Ebonyi kashedi za su iya rasa kujerunsu idan APC ta kunyata.
Mun rahoto Gwamna Francis Nwifuru yana cewa duk shugaban karamar hukumar da ya bari APC ta fadi zabe, ya yi ta kujerarsa bayan zaben 2027.
Kalamansa ba da 'yan adawa suke ba, amma ya saba doka kuma ya nuna yadda siyasa ta rufe ido.
5. Francis Fadahunsi
Gabanin zaben gwamna da aka yi a watan Agustan 2026, an ji yadda Francis Fadahunsi ya fito yana barazana ga rayukan ‘yan jam’iyyar Accord a Osun.
An zargi sanatan Gabashin Osun da bada umarnin a kashe ‘yan adawar APC, amma ya kare kan shi da cewa an fassara kalaman na shi ne ba daidai ba.
6. Yahaya Bello
A tsakiyar shekarar nan Sahara Reporters ta rahoto Yahaya Bello yana cewa za su casa mutanen da ya kira abokan gabarsu a siyasar Kogi ta tsakiya.
Tsohon gwamnan bai ambanci sunan kowa ba, amma yi maganganu masu hadari yayin da ake murnar Tijani Lubabatu Ozavize ta zama lauya.
7. Monday Okpebholo
Wani gwamna a Najeriya a wannan bakin jeri shi ne Monday Okpebholo wanda ya yi wa Peter Obi gargadi game da shigowa jihar Edo ba da izininsa ba.
A kan haka BBC ta rahoto Femi Falana yana cewa maganar da gwamnan Edo ya yi ta ci karo da sashe na 33 da ta ba kowane ‘dan kasa damar yawo.
8. Nyesom Wike
Lokacin da za a yi takarar 2023, Nyesom Wike ya fito ya yi kalaman da ake ganin suna da hadari a Najeriya da ta ke karkashin tsarin damukaradiyya.
Idan aka dogara da rahoton Vanguard, za a ji yadda tsohon gwamnan Rivers ya kira wasu ‘yan siyasa kusan 30, yake cewa ana neman su ruwa a jallo.
9. Abdulmajid Danbilki Kwamanda
Abdulmajid Danbilki Kwamanda sai da ya shiga hannun DSS a 2024 lokacin da aka zarge shi da tada wa gwamnatin Abba Kabir Yusuf hatsaniya.
Fitaccen ‘dan siyasar ya zargi Rabiu Kwankwaso a lokacin da yin kutun-kutun na ganin Muhammadu Sanusi II ya dawo kan ragamar sarkin Kano.
10. Adamu Aliyu Kibiya
Da ake tsoron Abba Kabir Yusuf zai iya rasa mulkin Kano a sakamakon hukuncin kotun karar zabe, Adamu Aliyu Kibiya ya fito ya yi baram-barama.
Da jin Adamu Aliyu Kibiya ya aika wa alkaklan kotun korafin zabe da barazanar kisa, wannan ya sa Gwamnan Kano ya yi maza ya tsige shi a 2023.

Kara karanta wannan
Shin da gaske Sheikh Gumi ya yi barazanar hargitsa Najeriya kan 'yan bindiga? An gano gaskiya
'Yan siyasa da kalamansu suka zama matasala a baya
11. Mukhtar Ramalan Yero
Mai girma Mukhtar Ramalan Yero ya yi maganganu marasa dadin ji kafin a yi zaben gwamnan Kaduna a 2015 lokacin da zai gwabza da Nasir El-Rufai.
The Guardian ta ce Ramalan ya yi wa magoya bayan APC da ‘dan takaransu barazanar hana shi shiga Kaduna ko ya rusa gidajensa ko ya hana shi motsi a jihar.
12. Ibrahim Shehu Shema
Gwamna Ibrahim Shehu Shema yana sahun wadanda ake zargi sun nemi tada rigima da suka hango jam’iyyar APC za ta iya kifar da su a zaben 2015.
Gwamnan Katsina ya kamanta ‘yan adawa da kyankyasai a gida ya kuma zuga mutane su kashe su kamar kwari a gidajensu, labarin ya zo a Vanguard.

Source: Getty Images
Majalisar shari'a ta yi zancen El-Rufai
Rahoto ya zo cewa Majalisar shari’a ta ce dole a yi wa Nasir El-Rufai adalci a shari’arsa da ICPC da DSS da ake yi a kotu dabam-dabam.
A wani jawabi da ta fitar ta hannun Nafiu Baba Ahmad, ta ce ya kamata a yi wa tsohon gwamnan Kaduna adalci kamar kowane 'dan kasa.
Sakataren Majalisar Shari’a ta SCSN ya bayyana damuwa kan tsare Nasir El-Rufai da ake yi har gobe
Asali: Legit.ng



