'Dole Ku Kawo Yankunanku ga APC': Gwamna Ya Yi Barazana ga Ciyamomi
- Gwamnan Ebonyi, Francis Nwifuru, ya umarci sababbin shugabannin ƙananan hukumomi su tabbatar APC ta lashe yankunansu
- Nwifuru ya ce ba barazana yake yi wa jam’iyyun adawa ba, sai dai ya tabbatar da cewa APC za ta yi nasara a dukkan zaɓukan jihar
- Gwamnan ya kuma bukaci shugabannin su sasanta da abokan hamayyarsu, yayin da ya nemi a ba mata da matasa damar samun naɗin mukaman gwamnati
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.
Abakaliki, Ebonyi - Gwamnan Ebonyi, Francis Nwifuru, ya ba sababbin shugabannin ƙananan hukumomin jihar kan zaben 2027.
Nwifuru ya umarci ciyamomin da aka rantsar da su su tabbatar APC ta lashe yankunansu a babban zaɓen 2027.

Source: Facebook
Gwamnan ya bayyana hakan ne yayin bikin rantsar da su bayan zaɓen ƙananan hukumomi da aka gudanar ranar 22 ga Agusta 2026, cewar Vanguard.
Barazanar da Gwamna Nwifuru ya yi
Ya ce duk shugaban ƙaramar hukumar da ya gaza tabbatar da nasarar APC a yankinsa a zaɓen 2027 za a cire shi daga mukaminsa.
Nwifuru ya bayyana cewa umarnin nasa ba barazana ba ce ga jam’iyyun adawa, sai dai nuna jajircewarsa wajen kare APC da tabbatar da nasararta.
A zaɓen, APC ta lashe dukkan kujerun shugabannin ƙananan hukumomi 13 da kuma kujerun kansiloli 171 da aka fafata a jihar.
Nwifuru ya ce yayin da aka fara yakin neman zaɓen kujerun Majalisar Dokoki ta Ƙasa, ana sa ran shugabannin za su tattara goyon bayan jama’a domin APC.
Ya ce:
“Ba za mu bar ko kujera ɗaya ga wata jam’iyyar siyasa ba. Za mu lashe kashi 100 cikin 100 na babban zaɓe. Ku je ku gaya wa ‘yan adawarmu cewa babu wanda ke yi musu barazana.”

Source: Original
Alfaharin da Gwamna Nwifuru ya yi kan zaɓe
Nwifuru ya ce an fara yakin neman zaɓe kuma APC ba za ta yi wa abokan hamayya barazana ba, sai dai za ta kayar da su a rumfunan zaɓe.

Kara karanta wannan
"Gwamnatinmu ce"; Kwamishina ya yi barazanar guntile 'yan yatsun masu adawa da APC
Gwamnan ya yi gargaɗin cewa duk shugaban ƙaramar hukumar da ya gaza kawo nasara wa APC a yankinsa zai fuskanci cirewa daga mukaminsa.
Ya ce:
“Yanzu mun fara yakin neman zaɓe. Ba barazana muke yi muku ba; za mu kayar da ku a rumfunan zaɓe. Babu wanda ke yi muku barazana. Mu ‘yan siyasa ne. Dole ne mu yi wa jam’iyyarmu magana kuma mu tabbatar da nasarar jam’iyyarmu.
“Idan muka yi nasara, kuma kun san za mu yi nasara, za mu cire duk shugaban ƙaramar hukumar da bai lashe ƙaramar hukumarsa ba. Hakan ne kawai.”
Sai dai ya umarce su da su tattauna da abokan hamayyarsu tare da sasanta da mutanen da suka fafata da su a zaɓen ƙananan hukumomi, cewar Daily Post.
Gwamnan ya kuma shawarci shugabannin da kada su ɗauki abokan gabansa a matsayin abokan gaba, yana mai cewa ba lallai ne abokin gabansa ya zama nasu abokin gaba ba.
Dan minista ya zama ciyaman a Ebonyi
An ji cewa Osborn Nweze Umahi, ɗan Ministan Ayyuka David Umahi mai shekaru 28, ya zama zababben shugaban ƙaramar hukuma.

Kara karanta wannan
Daraktan yakin neman zaben Tinubu, Abdulaziz Yari ya yi magana kan dawo da tallafin fetur
Umahi ya yi takarar kujerar shugaban Ohaozara ƙarƙashin APC, inda ya yi alkawarin fifita gaskiya, ingantaccen aiki da samar da ci gaba.
Bayan nasararsa, Umahi ya sha alwashin barin albashi da alawus ɗinsa gaba ɗaya, tare da mai da hankali kan ci gaban matasa.
Asali: Legit.ng
