Mutane fiye da 10 da Adeleke Ya Tara Wuri Daya Ya Yi Masu Duka a Zaben Osun

Mutane fiye da 10 da Adeleke Ya Tara Wuri Daya Ya Yi Masu Duka a Zaben Osun

Osun - Ta tabbata cewa Sanata Ademola Nurudeen Jackson Adeleke ya sake yin nasara a zaben gwamnan jihar Osun da ka yi.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

M Malumfashi ya shafe shekaru 10 yana kawo labaran Hausa musamman na siyasa, addini, tarihi, wasanni da al’ada

Wannan karo, ya ci zabensa ne a karkashin Accord Party, jam’iyya ta uku da ya tsaya takara a karkashinta a cikin shekaru tara.

Gwamnan Osun
Davido rungume da Gwamnan Osun Hoto: AAdeleke_01/x
Source: Twitter

'Yan APC da Adeleke ya ba kunya

Rahoton nan namu ya tattaro ‘yan siyasar da suka tsaya layi dabam da gwamnan da niyyar su ga bayan shi, shi kuma ya kai su kasa.

1. Bola Tinubu

Daily Trust ta ce cikin mutanen da aka doke duk ba su shiga takarar kai-tsaye ba akwai shi kan Mai girma shugaban kasa.

An yi tunanin tun da yana da alaka da jihar Osun kuma a matsayinsa na shugaban kasa, Bola Tinubu zai jawo APC ta karbe mulki.

Kara karanta wannan

Zaben Osun: Aikin Davido da abubuwa 5 da suka taimaki Adeleke ya sake doke APC

2. Bola Oyebamiji

Limamin shan kashi a zaben da aka yi shi ne Bola Oyebamiji wanda Ademola Adeleke ya doke shi da tazarar kuri’u 66, 252.

Ban da dukiya da ya rasa, abin da ya fi ciwo a takarar da ya yi shi ne ajiye mukaminsa da ya yi a NIWA domin neman gwamna.

3. Monday Okpebholo

Gwamnan Edo, Monday Okpebholo, ya tsokano wa kan shi fada lokacin da ya zargi Adeleke da yawan tika rawa har ya manta da aikinsa.

Bayan kwanaki takawaran nasa ya masa martani, yana sukar sunansa, kuma ya yi masa shagube dangane da sakamakon jarabawarsa ta WAEC.

4. AbdulRahman AbdulRazaq

Shi Gwamnan Kwara wanda shi ne shugaban gwamnonin jihohi ya fito yana cewa Osun na bukatar gwamna mai kusanci da Bola Tinubu.

Tun daga wajen Davido ya fara shan suka mara dadi. Mawakin ya ce kusancin wasu jihohin kasar nan da Tinubu bai kara masu komai ba.

Kara karanta wannan

Bayan tumurmusa shi a zabe, Gwamna Adeleke ya aika sako ga dan takarar APC

5. Hope Uzodinma

Gabanin zabe aka ji Hope Uzodimma yana fada wa Davido ya shirya daukar kawunsa aiki, yana nufin zai rasa kujerar gwamna.

Premium Times ta rahoto mawakin yana maida martani, ya zargi wani daga jihar Imo da kokarin kawo matsala a zaben jihar Osun.

6. Olagunsoye Oyinlola

Daf da zabe aka ji The Cable ta ce Olagunsoye Oyinlola ya fito ya mara wa APC baya, an yi mamakin jin hakan daga tsohon ‘dan PDP.

Duk da ya guji tsohon ‘dan jam’iyyarsa, goyon bayan Oyinlola da yaransa ba ta jawo masa komai ba illa shan kunya tun a rumfar zabensu.

7. Ajibola Basiru

Yadda jam’iyyar Accord ta doke Oyinlola a karamar hukumar Okuku, kusan haka aka yi wa Ajibola Basiru a zaben gwamnan na 2026.

Sakataren APC na kasa ya kawo akwatin rumfarsa da tazarar kuri’u 117 a Osogbo amma bai iya sa Oyebamiji ya zama gwamna ba.

8. Bisi Akande

Kara karanta wannan

Akuya ta zama silar arzikin Sanata Dino Melaye har ta kai ya mallaki motoci 200

Bisi Akande tsohon gwamna ne a Osun kuma wanda ya fara rike shugabancin APC, ba zai ji dadin sukuwar da Adeleke ya yi masu ba.

The Sun ta ce Baba Omokeekeeke ya iya jagorantar jam’iyyarsa ta samu kuri’u 181 inda yake zabe a Ila-Orangun a karamar hukumar Ila.

9. Francis Adenigba Fadahunsi

Gabanin zaben gwamna a Osun aka rahoto cewa Francis Adenigba Fadahunsi ya yi umarni a kashe ‘ya ‘yan jam’iyyar Accord mai mulki.

Sanatan ya karyata zargin inda ya ce an juya maganarsa wajen fassara. Za a sa shi cikin wadanda suka ji babu dadi a zaben da aka yi.

10. Sauran gwamnonin APC

Gwamnonin jihohin APC da dama sun tafi jihar Osun saboda su ga jam’iyyarsu ta raba Ademola Adeleke daga kan karagar mulki.

Osun: Ragowar wadanda suka sha kashi

A shafin Facebook, Babafemi Ojudu ya jero wasu mutane da ya ce su ne suka jawo jam’iyyar Accord ta doke APC a zaben jihar Osun.

Sanata Ojudu ya ambaci wasu ‘yan APC da yake ganin ba su taimaki jam’iyyar ba tare da yaba wa namijin kokarin Ademola Adeleke.

Kara karanta wannan

Zaben Gwamna: Abubuwa 5 da za su iya taimakon APC ta karbe jihar Osun

11. Hukumar EFCC

EFCC ta rufe asusun gwamnatin Osun lokacin da awanni suka rage a shiga zaben gwamna amma daga baya Bola Tinubu ya sa baki.

12. Gboyega Oyetola

‘Dan siyasar ya zargi ministan tarayyar da tsaida ‘dan takaran gwamna mara farin jini a APC wanda a karshen hakan ya ba gwamna mai-ci tazarce.

13. Hon. Wole Oke

Tsohon hadimin na marigayi Muhammadu Buhari ya kawo sunan Wole Oke wanda duk inda ya je sai ya tuna wa mutane Tinubu ne a mulki.

14. Ero Arike

Ojudu ya na da ra’ayin cewa Falilat Yusuf da ta fi shahara da Ero-Arike ta cuci APC da tsine-tsine da surutan da ta rika yi da sunan yakin zabe.

Yadda Adeleke ya lashe zabe a Osun

Rahoton nan ya yi nazarin irin yadda ayyukan Gwamna Ademola Nurudeen Jackson Adeleke suka ceci shi a zaben bana.

Dabarun siyasarsa da kuma rikicin APC sun taka rawar gani wajen kashin Asiwaju Munirudeen Bola Oyebamiji a jihar Osun

Ademola Adeleke ya ga bayan Asiwaju Munir Bola Oyebamiji da Najeem F. Salaam na APC da ADC da wasu ‘yan takara 13.

Asali: Legit.ng

Authors:
Muhammad Malumfashi avatar

Muhammad Malumfashi (Hausa writer) M. Malumfashi ya samu Digirin farko a ilmin komfuta a ABU Zaria. Baya ga haka ya yi Digirgir a fannin kula da bayanai da wani Digirgir a ilmin aikin jarida duk daga jami'ar. Malumfashi ya kan kawo labaran siyasa, addini, wasanni da al’ada. Ya halarci taron karawa juna sani iri-iri. Imel: muhammad.malumfashi@corp.legit.ng