Davido Ya Tafka Katobara, Lauya Ya Nuna Kuskuren Babban Mawaki
- Lauya Timothy Tugbiyele ya bukaci mawakin Afrobeats, Davido, da ya ba Gwamnan Edo, Monday Okpebholo, hakuri kan wallafa sakamakon WAEC da ake zargin na gwamnan ne
- Tugbiyele ya ce bai kamata Davido ya mayar da martani da kansa ga kalaman gwamnan ba, domin ya kamata Gwamna Ademola Adeleke ko wani jami’in gwamnatinsa ya mayar da martanin
- Lauyan ya ce siyasa bai kamata ta koma cin mutunci ba, inda ya bukaci Davido ya nuna tawali’u ya kuma nemi afuwar Okpebholo
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi
Jihar Osun - Wani lauya kuma marubuci, Timothy Tugbiyele, ya bukaci mawakin Afrobeats David Adeleke, wanda aka fi sani da Davido, da ya ba Gwamnan Jihar Edo, Monday Okpebholo, hakuri.
Lauyan ya bukaci Davido ya bayar da hakurin ne kan wani sakamakon jarabawar WAEC da ya wallafa a shafinsa na sada zumunta.

Source: Instagram
Jaridar The Punch ta ce Tugbiyele ya yi wannan kiran ne a wani bidiyo yayin da yake tsokaci kan rikicin siyasar da ake fama da shi gabanin zaben gwamnan jihar Osun da za a gudanar ranar 15 ga Agustan 2026.
Davido ya yi wa gwamna shagube
A ranar Juma’a ne Davido ya wallafa abin da ya bayyana a matsayin sakamakon WAEC na Okpebholo, jim kadan bayan gwamnan Edo ya yi wa Gwamnan Osun, Ademola Adeleke, ba’a kan yadda yake yawan rawa.
Okpebholo ya soki salon shugabancin Adeleke ne yayin da yake yakin neman zaben dan takarar jam’iyyar All Progressives Congress (APC), Bola Oyebamiji, wanda aka fi sani da AMBO.
Bayan kalaman, Davido, wanda ke fafutukar ganin kawunsa Adeleke ya samu wa’adi na biyu, ya wallafa sakamakon WAEC da ake zargin na Okpebholo ne ba tare da wani rubutu a kai ba.
Okpebholo ya cancanci a nemi afuwarsa

Kara karanta wannan
Abu ya girma: An tura saƙo ga Amurka da Birtaniya don su hukunta sanatan Najeriya
Da yake magana kan lamarin, Tugbiyele ya ce bai kamata Davido ya mayar wa gwamnan martani da kansa ba.
“Na kalli wani bidiyo lokacin da Gwamna Okpebholo ya kira gwamnan jihata, Adeleke, gwamnan rawa. Sai dan uwan gwamnan, David Adeleke, ya mayar da martani ta hanyar wallafa sakamakon WAEC na kammala makarantar sakandare na Gwamna Okpebholo, gwamnan Edo.” In ji shi
A cewar lauyan, duk da cewa sakamakon da ake zargin na Okpebholo ne bai yi kyau ba, bai kamata a yi amfani da shi wajen yi masa ba’a ba.
“Sakamakon bai yi kyau sosai ba, amma hakan na iya faruwa. Gwamnan ya sake rubuta jarabawar. Ba mu san da hakan ba, amma ina ganin wallafar Davido, David Adeleke, ba ta dace ba.” In ji shi
Adeleke ya kamata ya mayar da martani
Tugbiyele ya ce Adeleke zai iya mayar wa takwaransa na Edo martani ta hanyoyin hukuma maimakon barin Davido ya shiga tsakaninsu.
"Gwamna Adeleke, Ademola Adeleke, ya kamata ya mayar wa takwaransa gwamna martani, ko ya sa daya daga cikin ma’aikatansa, watakila kwamishinan yada labarai ko mai ba shi shawara na musamman, ya mayar da martani. Ba Davido, David Adeleke ba.” In ji shi.
Lauyan ya kuma jaddada cewa Davido da Okpebholo suna da matsayi daban-daban, don haka bai kamata su rika mu’amala da juna a matsayin masu matsayi iri daya ba.

Source: Facebook
"David Adeleke da gwamnan jiha ba su da matsayi iri daya. Ba su da matsayi guda. Ba su cikin aji guda.” In ji shi.
Tugbiyele ya bayyana wallafar Davido a matsayin rashin girmamawa, inda ya roki mawakin da ya ba Okpebholo hakuri.
"Ina ganin abin da Davido ya yi rashin girmamawa ne, kuma ina rokon sa da ya nuna tawali’u ya nemi afuwa.” In ji shi.
Shehu Sani ya yi wa Davido martani
A wani labarin kuma, kun ji cewa tsohon sanata kuma mai fafutukar kare hakkin dan Adam, Shehu Sani, ya yi watsi da kiran fitaccen mawakin Afrobeats, David Adeleke, wanda aka fi sani da Davido.
Sanata Shehu Sani ya yi watsi da kiran na Davido na neman Shugaban Amurka Donald Trump da kasashen duniya su sanya ido kan zaben gwamnan jihar Osun mai zuwa.
Asali: Legit.ng

