Latest
Rahotanni sun nuna cewa wasu 'yan bindiga masu garkuwa da mutane sun kai hari karamar hukumar Rogo a jihar Kano sun kashe mutum 1 sun jikkata wasu.
Aƙalla mutane uku da ake zargi da hannu a kisan basarake a Langtang North da ke Plateau State sun mutu bayan fusatattun matasa sun kama su tare da kona su da wuta.
Jami'an rundunar sojin Najeirya sun kama wani mutumi da ake zargin dan leken asirin kungiyar ta'addancin Boko Haram ne a filin jirgin sama a jihar Yobe.
Tsohon shugaban kasa, Olusegun Obasanjo zai jagoranci taron 'yan adawa a Najeriya a Ibadan jihar Oyo. Kwankwaso da sauran yan ADC sun isa Ibadan.
A labarin nan, za a ji cewa babban lauya a Femi Falana ya bayyana cewa an karya doka a shari'ar da gwamnati ke yi da sojojin da suka shirya kifar da Tinubu.
'Yan ta'addan kungiyar Boko Haram sun dasa bam a jihar Borno. Bam din ya jawo asarar rayukan mutanen da ba su san hawa ba, ba su san sauka ba, bayan ya tarwatse.
Jarumar fina-finai ta Kannywood, Mansurah Isah ta bayyana cewa za ta tallata shugaba Bola Tinubu a zaben 2027. Ta bayyana cewa mafi yawan 'yan Kannywood a APC suke.
Ministan lantarki, Bayo Adelabu, ya yi murabus daga gwamnatin shugaban kasa Bola Ahned Tinubu. Ministan ya yi murabus ne duk da Shugaba Tinubu bai so hakan ba.
Kakakin jam'iyyar ADC na kasa, Bolaji Abdulahi ya zargi jam'iyyar APC da shirya hana taron 'yan adawa a Ibadan. ADC za ta yi taron ne domin shirya tunkarar APC.
Masu zafi
Samu kari