Dubu Ta Cika: An Kama Wani Mai Taimaka Wa Yan Ta'adda a Filin Jirgin Sama a Jihar Yobe

Dubu Ta Cika: An Kama Wani Mai Taimaka Wa Yan Ta'adda a Filin Jirgin Sama a Jihar Yobe

  • Dakarun sojoji sun yi nasarar damke wani mutumi da ake zargin dan leken asirin kungiyar Boko Haram ne a filin jirgin sama na jihar Yobe
  • Rahoto ya nuna cewa bayan kama mutumin, sojoji sun mika shi sashen leken asiri na rundunar Operation Hadin Kai domin ci gaba da bincike
  • Wannan dai na zuwa ne yayin da hare-haren 'yan ta'addan Boko Haram da ISWAP ke karuwa a yankin Arewa maso Gabashin Najeriya

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Jihar Yobe, Nigeria - Jami'an rundunar sojin Najeriya sun cafke wani da ake zargin yana taimaka wa yan ta'adda da bayanan sirri a filin jirgin sama a jihar Yobe.

Dakarun rundunar Operation Hadin Kai ne suka samu wannan nasara, inda suka kama wanda ake zargi da ba ‘yan Boko Haram da ISWAP bayanai a filin jirgin sama na Muhammadu Buhari International Cargo Airport da ke jihar Yobe.

Kara karanta wannan

'Yan Boko Haram sun dasa bam a Borno, mutane da dama sun rasu

Dakarun soji.
Babban Hafsan Tsaron Najeriya, Janar Olufemi Oluyede tare da dakarun sojoji a wata ziyara da ya kai Maiduguri Hoto: @NigerianArmy
Source: Facebook

Masani kuma mai sharhi kan harkokin tsaro a Najeriya, Zagazola Makama ya tabbatar da hakan a shafinsa na X jiya Juma'a, 24 ga watan Afrilu, 2026.

Yadda aka kama wanda ake zargi

Rahotanni daga majiyoyin tsaro sun bayyana cewa an kama mutumin ne da misalin ƙarfe 5:30 na safiyar ranar Alhamis, 23 ga watan Afrilu, 2026.

Dakarun sashe na 2 na rundunar sojin Operation Hadin Kai da ke aiki a filin jirgin ne suka kama shi bayan sun lura da yadda yake zirga-zirga cikin shakku a kusa da sansanin soji.

Matakin da aka dauka bayan kama shi

Majiyoyin sun ce wanda ake zargin bai bayar da wani bayani mai amfani ba lokacin da aka fara yi masa tambayoyi tun a filin jirgin saman, lamarin da ya sa aka fara zarginsa.

Daga bisani dakarun sojojin sun miƙa shi ga sashen leƙen asirin soji domin ci gaba da gudanar bincike, kamar yadda jaridar The Cable ta ruwaito.

Kara karanta wannan

Al'umma sun samu saukin hare hare, hatsabibin dan ta'addan ISWAP ya bakunci lahira

Sojoji.
Dakarun sojojin Najeriya a baki aiki da wani dan lekem asirin Boko Haram da aka kama a Yobe Hoto: @ZagazolaMakama
Source: Twitter

An kuma bayyana cewa duk da cewa ana ganin zaman lafiyaya dawo a yankin a halin yanzu, amma har yanzu akwai rashin tabbas kan abin da ka iya zuwa ya dawo.

Sai dai jami’an tsaro na ci gaba da nuna ƙwarin gwiwa da ƙwarewa a aikin su wajen bincike da zakulo duk wanda ake ganin abin zargi ne game da matsalar tsaron da ake fama da ita.

A watan da ya gabata ma, dakarun soji sun kama wasu mutum biyu da ake zargin suna bai wa ‘yan Boko Haram da ISWAP bayanai a ƙaramar hukumar Damboa ta jihar Borno.

Sojoji sun kashe mayakan ISWAP 20

A wani labarin, kun ji cewa dakarun rundunar Operation Hadin Kai sun kashe aƙalla mambobi 20 na ƙungiyar Boko Haram/ISWAP, a jihar Yobe.

Daga cikin 'yan ta'addan da aka kashe har da wani kwamanda da aka bayyana matsayin Abu Yusu, Munzir na Dursula a Goniri da ke ƙaramar hukumar Gujba a jihar Yobe.

An samu wannan nasara ne yayin da ’yan ta’addan sun yi yunkurin kai hari kan sansanonin sojoji ne da ke ƙarƙashin Sassa na 2 na Operation Hadin Kai (OPHK).

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262