Iran Ta Kafa Tarihi a Duniya bayan Shiga Kwana na 57 a Yakinta da Isra’ila

Iran Ta Kafa Tarihi a Duniya bayan Shiga Kwana na 57 a Yakinta da Isra’ila

  • Kasar Iran ta shiga tarihin duniya bayan katse intanet na kwanaki 57 ba tare da tsayawa ba yayin da ake ci gaba da yaki
  • Katsewar ta fara ne bayan hare-haren haɗin gwiwa na Amurka da Isra’ila a Tehran, lamarin da ya keɓe ‘yan ƙasar daga duniya
  • Duk da matsin lamba da rikicin diflomasiyya da Amurka, Iran ta ƙi shiga tattaunawa kai tsaye, yayin da ake ci gaba da takaddama

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Tehran, Iran - Ƙasar Iran ta fuskanci katsewar intanet na tsawon kwanaki 57 ba tare da tsayawa ba a yakin da ake yi a Gabas ta Tsakiya.

Majiyoyi sun tabbatar da cewa hakan ya zama mafi tsawo a tarihin duniya a matakin ƙasa da aka taba yi.

Iran ta shafe kwanaki 57 ba tare da intanet ba
Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu da sabon jagoran addini a Iran, Mojtaba Khamenei. Hoto: Gil Cohen-Magen.
Source: Getty Images

Rahotanni daga Al Jazeera sun nuna cewa an fara katsewar ne bayan hare-haren haɗin gwiwa da Amurka da Isra’ila suka kai a Tehran a ranar 28 ga Fabrairu.

Kara karanta wannan

Hormuz: Matakin Amurka da Iran ya ta'azzara farashin fetur a duniya, ganga ta haura $100

Yadda yakin Iran da Isra'ila ya barke

Hakan na zuwa ne yayin da ake ci gaba da yaki tsakanin Iran da Isra'ila wacce ke samun goyon bayan Amurka karkashin jagorancin Donald Trump.

Yakin akalla ya kwashe mako uku kenan tun bayan harin farko a ranar 28 ga watan Fabrairun shekarar 2026 da muke ciki.

Harin ya yi sanadiyyar mutuwar jagoran addini a Jamhuriyar Musulunci ta Iran, Ayatollah Ali Khamenei da wasu manyan jami'an tsaro.

Ana ci gaba shan wahala a Iran kan rashin intanet
Shugaba Masoud Pezeshkian na Jamhuriyar Musulunci ta Iran. Hoto: Anadolu Ajansi.
Source: Getty Images

Yadda katse intanet ya shafi mutanen Iran

Majiyoyi suka ce katsewar ta hana muryoyin ‘yan ƙasar bayyana, ta raba iyalai da abokai, tare da jawo mummunar illa ga tattalin arziki.

Haka kuma, wannan mataki ya ware ‘yan Iran daga sauran duniya a lokacin da yankin ke cikin tashin hankali mai tsanani.

A wani ɓangare, rikicin diflomasiyya tsakanin Iran da Amurka ya ƙara tsananta, inda Iran ta dage cewa ba za ta shiga tattaunawa kai tsaye ba.

Kara karanta wannan

Yadda takaita intanet na kwanaki 54 a Iran ke jawo asara

Takaddama kan batutuwan nukiliya, bude mashigar Hormuz, da ayyukan soji na Isra’ila a Lebanon na ci gaba da hana cimma matsaya, cewar The Arabian Stories.

Yayin da Amurka ke ƙara ƙarfafa rundunarta da sanya takunkumi, Iran ma ta ɗauki matakan ramuwar gayya da suka shafi harkokin sufuri da kasuwanci.

Har yanzu dai ana cikin rashin tabbas kan ko za a ci gaba da tattaunawa, yayin da matsin lamba ke ƙaruwa a yankin Gabas ta Tsakiya.

Iran ta yankewa dan leken asiri hukuncin kisa

Mun ba ku labari a baya cewa hukumomin Iran sun zartar da hukuncin kisa kan wani mutum da ke yada bayanan sirrinta ga kasar Isra'ila da suke rikici.

An kama mutumin mai suna Mehdi Farid da laifin yi wa Isra’ila leƙen asiri tare da tura bayanan sirri ga Mossad yayin da ake ci gaba da yaki a yankin Gabas ta Tsakiya.

Rahotanni sun ce marigayin ya yi aiki a wani bangare mai matuƙar muhimmanci na tsaron farar hula, inda ya yi amfani da damar da yake da ita.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.