Yan fashi
'Yan bindiga sun hallaka shugaban al'ummar Fulani a wani yankin jihar Kaduna. Sun kama shugaban na Fulani ne suka kwantar suka yi masa yankan rago har lahira.
'Yan sanda a jihar Kaduna sun fatattaki 'yan bindiga tare kwato wasu muggan makamai da mota kirar Golf 3 daga hannun 'yan bindiga. An yi bata kashi a tsakani.
Wasu 'yan fashi sun yi wuf sun far wa wani kwastoman banki da nufin kwace masa kudade N10m. An jima ana daga tsakananin kwasatoman da 'yan fashin kafin a cecesh
'Yan bindiga sun budewa wasu mafarauta wuta a wani dajin jihar Katsina. Sun hallaka mutane har lahira yayin da suka yi awon gaba da mutane 17 daga cikinsu.
Shugaba Muhammadu Buhari ya nuna rashin jin dadinsa ga sabbin hare-hare da aka kai wasu sassan kasar a makon nan. Yace ba zai bari a lalata ilimi ba a kasar.
A jihar Zamfara, an kwana uku a jere a wani kauye 'yan bindiga na kai hari. 'An kashe mutane tare da sace kayayyakin gona da kuma kone gidaje masu yawa a yankin
'Yan bindiga a jihar Benue sun kashe wani dan sanda tare da kone ofishin 'yan sanda kurmus. Sun kuma kone wasu gidaje da dama da ba a tantance adadinsu ba.
Gwamnan jihar Neja ya bayyana asalin abinda 'yan bindiga ke yi na yaudarar gwamnati. Yace, suna tuban muzuru ne su karbi kudi su kara siyan muggan makamai.
'Yan bindiga sun kai hari unguwar ma'aikatan hukumar kula da jiragen sama sun yi awon gaba da mutum 11 da safiyar ranar Asabar. Rahotanni sun bayyana ba rauni.
Yan fashi
Samu kari