Labaran NNPC
Farashin man fetur ya fara komawa gidan jiya bayaj karewar yarjejeniyar cinikayya tsakanin gwamnatin tarayya da matatun mai a Naira, luta ta ƙara tsada a Legas.
Kungiyar 'yan kasuwar man fetur sun kara kudin litar man fetur a Najeriya. za a dawo sayar da litar mai a N900 a kan N890 da aka saba a makon da ya wuce.
Kamfanin NNPCL ya karyata cewa an kai hari matatar Fatakwal da ke jihar Rivers bayan Tinubu ya dakatar da Gwamna Simi Fubara. NNPCL ya ce matatar na aiki.
Rahotanni sun bayyana cewa Najeriya ta dakatar da sayar wa matatar Dangote danyen man fetur, wanda hakan zai shafi kasuwar man fetur a fadin Najeriya.
Kotun Tarayya ta yi zama kan ƙarar kamfanin NNPCL da ke ƙalubalantar cancantar karar da matatar Aliko Dangote ta shigar kan lasisin shigo da kaya a Abuja.
Farashin shigo da litar man fetur ya sauka a Najeriya. 'Yan kasuwa sun koka yayin da 'yan Najeriya za su samu sauki a harkokin kasuwanci da hada hadar yau da kullum.
Masana sun bayyana cewa, akwai yiwuwar man fetur ya koma N500 idan aka bi wasu hanyoyi masu sauki a kasar. Sun bayyana hakan ne tare da hango mafita ga kasa.
Yan kasuwar man fetur sun bayyana cewa za su sauke farashin man fetur kasa da na matatar Dangote. Hakan na zuwa ne bayan mai ya sauka a kasuwar duniya.
Kungiyar dillalan mai ta PETROAN ta nemi a kafa doka da za ta kayyade sauya farashi zuwa sau daya cikin watanni shida domin hana rashin tabbas a kasuwa.
Labaran NNPC
Samu kari