Biki Bidiri: Fitaccen Jarumin Kannywood, Adam A. Zango Ya Yi Sabon Aure a Kasar Waje

Biki Bidiri: Fitaccen Jarumin Kannywood, Adam A. Zango Ya Yi Sabon Aure a Kasar Waje

Kaduna, Nigeria - Fitaccen jarumin masana'antar shirya fina-finai ta Kannywoos, Adam. A. Zango ya yi sabon aure kwanaki kadan bayan rabuwa da tsohuwar matarsa.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Wannna aure na Jarumin na zuwa ne bayan aurensa da jarumar Kannywood, Maimuna Musa, wacce aka fi sani da Maimuna Pretty ya mutu.

Adam A. Zango.
Fitaccen jarumin Kannywood, Adam A. Zango d sabuwar amaryarsa Hoto: Adam. A. Zango
Source: Facebook

Adam A. Zango ya tabbatar da cewa ya yi sabon aure a wani gajeren sako mai dauke da hotonsa da na amaryarsa da ya wallafa a shafinsa na Facebook.

Rahotanni sun nuna cewa fitaccen jarumin na Kannywood, Adam A. Zango, ya sake yin aure ne a ƙasar Nijar.

Bayan kammala bikin, jarumin ya bayyana godiyarsa ga Allah, tare da aika saƙo ga masu nuna baƙin ciki kan sabon aurensa da cewa: “Ku ci kanku.”

Karin bayani na nan tafe...

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262