Labaran Duniya
Shekarar 2020 ta zo wa ‘yan Najeriya da ban mamaki iri-iri. Mun tattaro maku wasu daga cikin manyan labaran irinsu shigo Najeriya da COVID-19a farkon bana.
An yanke wa wani mutumin kasar Faransa hukuncin daurin shekara biyar a gidan kurkuku saboda samunsa da laifin harbe wani zakara saboda ya dame shi da cara.
A jiya ne Gwamnatin kasar Amurka ta fito ta na zargin Najeriya da muzguna wa mutane saboda addinsu. Amurka ta ce babu ‘yancin mutum ya yi addinin da yake so.
Za ku ji cewa Mabarata a jihar Kano sun fada ragar Hisbah bayan Dr. Abdullahi Ganduje ya haramta bara. Khadimul Islam ba ya shiri da masu wannan danyen aiki.
Muhammadu Buhari ya kaddamar da wani aikin wutar lantarki a makarantar Arewacin Najeriya. FUAM ce Makaranta ta biyu bayan BUK da aka hada wa wannan tashar.
Mun ji cewa da alamu Donald Trump ya saduda, ya fara maganar dawowa siyasa a 2024. Trump ya ce ya na neman tazarce, amma idan bai yiwu ba, zai dawo nan gaba.
‘Yan Majalisa sun yi muhawara game da bashin Ganduje, sun amince a aro kudi. Abdullahi Umar Ganduje ya ce za ayi amfani da wannan kudi ne domin ayi ayyuka.
Wata yar kasar China mai suna Zhao mai shekara 31 da aka yi wa tiyatar sauya hanci ta yi matukar kaduwa bayan ta gano an gutsure mata kunne ba da izininta ba.
Alhaji Lai Mohammed, wanda ya bayyana dawowa da gunkin a matsayin somin taɓi, ya ce baya ga ɗimbin moriyar da za'a samu, waɗannan kayayyakin tarihi na nuni da
Labaran Duniya
Samu kari