Jerin labaran da suka ratsa gari daga watan Junairu zuwa Disamban bana

Jerin labaran da suka ratsa gari daga watan Junairu zuwa Disamban bana

Shekarar 2020 ta zo wa ‘yan Najeriya da ban mamaki iri-iri. Mun tattaro maku wasu daga cikin manyan labaran da su ka ratsa ko ina a shekarar bana.

Legit.ng Hausa ta tsakuro wasu daga cikin wannan rubutu daga jaridar nan ta The Nation.

1. Shigo da COVID-19

A ranar 25 ga watan Fubrairu ne aka sami wani mutumin kasar Italiya da ya shigo Najeriya dauke da kwayar cutar COVID-19, wannan labari ya tada hankalin ‘yan kasar.

2. Mutuwar Abba Kyari

Jim kadan bayan nan sai aka ji cewa Malam Abba Kyari ya kamu da Coronavirus. A ranar 17 ga watan Afrilu, 2020 ne hadimin shugaban kasar ya rasu a sakamakon jinya.

COVID-19 ta yi sanadiyyar mutuwar Buruji Kashamu da Abiola Ajimobi da wasu manya a bana.

3. Fyade

A shekarar nan an yi ta samun munanan labaran fyade, a haka ne aka tsinci gawar Uwaila Omozuwa a wani coci a garin Edo bayan zargin an yi lalata da ita kafin nan.

An kuma samu wata ‘yar makaranta a Ogun, Grace Oshiagwu da aka yi lalata da ita, har ta mutu.

KU KARANTA: Tsohon Ministan Najeriya, Ismaila Funtua ya mutu

4. Mace-mace a Kano

Daga watan Afrilu ne aka rika samun labaran mace-mace rututu a jihar Kano. Ana zargin mutane fiye da 1000 sun mutu ba tare da an tabbatar da abin da ya kashe su ba.

5. Zanga-zangar #EndSARS

A wannan shekara ne aka yi gagarumar zanga-zangar #EndSARS wanda ya tada jihohin Najeriya. Wannan zanga-zanga da aka yi wa ‘yan sanda ya rikide ya zama tada tarzoma.

Wasu gungun matasa daga Arewacin Najeriya sun fito da na su salon mai taken #SecureNorth.

6. Boko Haram

A wannan shekara an fuskanci hare-haren ‘yan ta’addan Boko Haram, daga ciki akwai kisan matafiya da aka yi a garin Auno, da kisan wasu manoma a Zabarmari, Borno.

7. Garkuwa da mutane

A bana garkuwa da mutane ya yi kamari musamman a Arewacin Najeriya, daga cikin wadanda aka yi garkuwa da su har da wasu manyan ‘yan siyasa, wasu sun mutu a dalilin haka.

8. Yajin-aikin ASUU da NLC

A farkon shekarar nan ne kungiyar ASUU ta tafi yajin-aiki, watanni tara kenan da rufe jami’o’in gwamnati. Kungiyar NLC ma ta yi barazanar zuwa yajin-aiki, amma daga baya ta fasa.

Jerin labaran da suka ratsa gari daga watan Junairu zuwa Disamban bana
Masu zanga-zangar EndSARS Hoto: www.thecable.ng
Asali: UGC

KU KARANTA: Lekki: Gwamnan Legas ya bayyana wanda su ka yi harbe-harbe

9. Karin farashin man fetur

A 2020 ne farashin man fetur ya yi tsadan da bai taba yi ba, gwamnatin tarayya ta kai kudin litar mai har zuwa N168-N172 a sakamakon janye tallafin man fetur da aka yi kwanaki.

10. Sauyin kudin lantarki

Wani babban labari a bana shi ne karin kudin wutar lantarki, wasu sun gamu da kusan karin 50%.

Tun watan Maris, abu yaci tura game da yajin-aikin ASUU. Ministan kwadago, Chris Ngige yace sai kungiyar malaman ta janye yajin-aiki, za a fito mata da kudinta.

Wankin hula ya kai gwamnati dare tun kungiyar ASUU ta ki janye dogon yajin-aikin da ta shafe watanni tara tana yi.

Idan ku na da wata shawara ko bukatar bamu labari, tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Asali: Legit.ng

Online view pixel