Jihar Kogi
Ministan Ayyuka a Najeriya, David Umahi, ya bai wa masu kwangilar gyaran hanyar Abuja zuwa Lokoja wa'adin sa'o'i 72 su koma aiki ko su fuskanci EFCC.
‘Yan bindiga sun kashe wani jami’in hukumar NSCDC, Ayo Olukotun, tare da sace diyarsa da wasu mutane bayan kai hari garin Odo-Ere da ke jihar Kogi.
Dakarun sojin Najeriya sun dakile shirin garkuwa da mutane a Kogi, sun kashe dan ta’adda tare da kwato makamai da harsasai masu yawa bayan musayar wuta mai tsanani.
Rahotannin da muke samu sun tabbatar da cewa wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne sun tare dillalan dabbobi daga Ajingi a Kano tare da sace raguna 11 yayin zuwa Kogi.
Tsohon gwamna, Yahaya Bello da Sanata Sunday Karimi na cikin ’yan takarar da kwamitin tantance APC ya amince su fafata a zaɓen fidda gwani na sanatoci a Kogi.
A Najeriya, an fara shirye-shiryen zabukan shekarar 2027 wanda ake ganin zai zama daban da sauran zabukan da aka yi a shekaru musamman wasu na sanatoci a Arewa.
Sarkin da aka sace a jihar kogi, Adebayo Samuel ya rasu a cikin daji bayan kwanaki a hannun masu garkuwa da mutane. Mutane sun shiga jimami a garinsu.
Mutane 16 sun rasu a hatsarin motar bas daga Jos zuwa Legas a ranar 8 ga Mayu, 2026, a Osara jihar Kogi, sakamakon gudun wuce sa'a da direba ya yi.
Rayuka sun salwanta a rikicin fili tsakanin Itale da Ishi a jihar Kogi ranar 7 ga Mayu, 2026, yayin da ƴan sanda suka tura jami'an haɗin gwiwa don tabbatar da tsaro.
Jihar Kogi
Samu kari