Zaben 2027: Aisha Yesufu Ta Janye daga Neman Takarar Sanata a Jam'iyyar NDC

Zaben 2027: Aisha Yesufu Ta Janye daga Neman Takarar Sanata a Jam'iyyar NDC

  • 'Yar gwagwaarmayar kare hakkin bil'adama, Aisha Yesufu ta janye daga neman takarar sanata mai wakiltar Abuja a Majalisar dattawa
  • Hakan ya biyo bayan tsarin da jam'iyyar NDC ta amince da shi na fitar da 'dan takarar sanata ta masalaha, ba tare da shirya zaben fitar da gwani ba
  • Aisha ta bukaci magoya bayanta su kwantar da hankulansu, su maida hankali kan babban aikin da ke gabansu na ceto Najeriya

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Abuja, Nigeria - Fitacciyar mai fafutukar kare hakkin jama’a kuma mai sharhi kan harkokin siyasa, Aisha Yesufu, ta sanar da janyewarta daga takarar kujerar Sanata mai wakiltar Babban Birnin Tarayya (FCT).

'Yar gwagwarmayar ta tabbatar da cewa ta hakura da neman taiarar sanata a karkashin jam’iyyar NDC gabanin babban zaben shekarar 2027.

Aisha Yesufu ta bayyana matakin nata ne cikin wata sanarwa da ta wallafa a shafinta na X ranar Juma’a, 29 ga watan Mayu, 2026.

Kara karanta wannan

"A maido mani da kudi na," Matar da ta fito takarar shugaban kasa ta tada rigima a DLA

Ta ce jam’iyyar NDC ta yanke shawarar ba za ta gudanar da zaben fitar da gwani na kujerar Sanata a Abuja ba, wanda hakan ya sa ta janye daga shiga tseren neman tikiti.

“Jam’iyyarmu ta yanke shawarar ba za ta gudanar da zaben fitar da gwani na kujerar Sanata a Abuja ba. Sai dai za ta gudanar da na kujerun majalisar wakilai. Don haka ku ci gaba da bayyana ra’ayinku,” in ji ta.

Aisha Yesufu ta aika sako ga magoya baya

Mai fafutukar ta bukaci magoya bayanta da su ci gaba da nuna hakuri tare da mayar da hankali kan abin da ta bayyana a matsayin babban burin ceto Najeriya a zaben shugaban kasa na 2027.

Ta ce:

“Ina rokon kowannenku da ku kwantar da hankalinku sannan ku mayar da hankali kan babban burin da muka sa a gaba, wato zaben shugaban kasa. Najeriya za ta samu sauyi mai kyau.”

Aisha Yesufu ta kuma gode wa magoya bayanta na #AishaForSenate bisa goyon baya da jajircewar da suka nuna tun bayan bayyana aniyarta ta shiga takarar.

Ta kuma bayyana cewa a cikin mako mai zuwa za ta zagaya dukkanin kananan hukumomin yankin Abuja guda shida domin gode wa al’umma bisa irin tarbar da suka yi mata.

Kara karanta wannan

Zargin fyade" ADC ta fara bore bayan kotu ta tasa 'keyar da takararta zuwa kurkuku

Yadda ta shiga takarar

Tribune Nigeria ta ruwaito cewa Aisha Yesufu ta bayyana aniyarta ta neman kujerar Sanatan Abuja ne a ranar 6 ga watan Mayu bayan ta sauya sheka daga jam’iyyar ADC zuwa NDC.

A lokacin, ta bayyana cewa gogewarta a siyasa da kuma rawar da take takawa a cikin jam’iyyar ne suka karfafa mata gwiwar shiga takarar.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262