Fulani Makiyaya
Akalla mutane uku ne suka rasa ransu, tare da barnar makudan dukiya a yayin wani kazamar rikicin kabilanci daya barke tsakanin al’ummar Fulani da kabilun Tibabe a kauyen Pangari na karamar hukumar Bali na jahar Taraba.
Wani yaro mai shekaru 15 a duniya dan Fulani mai kiwon shanu ya gamu da sharrin miyagu a lardin Kukum dake cikin masarautar Kagaro na karamar hukumar Kaura a jahar Kaduna, inda suka kashe shi yayin da yake kan hanyarsa ta komawa g
Kaakakin gwamnan jahar, Chibuike Onyeukwu ne ya bayyana haka cikin wata sanarwa daya fitar inda yace kungiyar mai suna ‘South East Youth Leaders’ ba ta da hurumin yin magana da yawun al’ummar jahar ko gwamnatin jahar.
Wata kotun majistri dake zamanta a jahar Kwara ta bayar da umarnin garkame wani matashi bafulatani, Iliyasu Abubakar a kurkukun gwamnatin tarayya dake garin Ilorin saboda tuhumarsa da ake yi da halaka dan uwansa.
Wata shugabar Fulani ta bayyana gagarumar gudumuwar da Makiyaya su ke badawa a kasar nan inda ta fadi mataki daya da Fulani za su dauka ‘Yan Najeriya su dandana kudarsu.
Gwamnan jahar Katsina, Aminu Bello Masari ya gayyaci shuwagabannin al’ummar Fulani dake zaune a kananan hukumomi guda 9 na jahar Katsina domin tattauna hanyar kawo karshen matsalolin tsaro a jahar.
Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya bayyana abin da ya ware domin aikin RUGA. Ita Enang ya ce Gwamnatin nan ta kasafta Biliyan 2.2 domin aikin RUGA a fadin Najeriya a wannan shekara ta 2019.
Mun kawo maku abin da Olusegun Obasanjo ya fada bayan ya gana da Fulani. Za ku ji batutuwan da tsohon Shugaban kasa Obasanjo ya yi magana a kai a lokacin da a ka yi wani zama jiya.
Gwamnati jihar Zamfara ta dakatar da shugaban karamar hukumar Maradun, Ahmad Abubakar, bayan ta zarge shi da nuna halin ko in kula wajen kawo zaman lafiya a yankin. Kamfanin dillancin labarai na Najeriya (NAN) ya ruwaito cewa...
Fulani Makiyaya
Samu kari