'Yan Bindiga Sun Yi Wa Jami'an Tsaro Kofar Rago, an Rasa Rayuka a Musayar Wuta
- Wasu ‘yan bindiga sun yi kwanton bauna ga jami’an tsaro da ke sintiri a karamar hukumar Riyom ta jihar Plateau
- Rahotanni sun nuna cewa maharan sun kashe jami’an tsaro biyu tare da kwace bindigoginsu a yayin harin
- Jami’an tsaro sun kaddamar da bincike da sintiri a kauyukan da ke kusa domin gano maharan da suka kawo harin
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Sani Hamza ƙwararren edita ne a fannin nishaɗi, al'amuran yau da kullum, da kuma siyasa, wanda ke da shekaru sama da takwas a aikin jarida
Jos, Plateau - Wasu ‘yan bindiga sun yi kwanton bauna ga jami’an tsaro da ke sintiri a kan wata hanya a jihar Plateau.
'Yan bindigan sun farmaki jami'an tsaron ne a kan hanyar Ganawuri zuwa Sabon Gida da ke karamar hukumar Riyom ta jihar Plateau.

Source: Original
Rahoton Vanguard ya nuna cewa ‘yan bindigar sun kashe jami’an tsaro biyu tare da kwace bindigoginsu na aiki.
Majiyoyin tsaro sun bayyana cewa lamarin ya faru ne da safiyar ranar Talata, 4 ga watan Agustan 2026 lokacin da jami’an tsaro hudu daga wurare biyu daban-daban suka kafa shingen bincike a kan hanyar.

Kara karanta wannan
'Yan ta'addan Lakurawa sun kai hari a Sokoto, an kashe jami'an tsaro da fararen hula
Yadda 'yan bindiga suka kai harin
Majiyoyin sun ce bayan kammala aikin, jami’an sun kama hanyar komawa wuraren aikinsu daban-daban.
Sai dai jami’ai biyu ba su koma ba, lamarin da ya sa takwarorinsu suka fara bincike domin gano inda suke.
Daga bisani, an gano gawarwakin jami’an biyu a wurin da aka kai harin, yayin da aka tabbatar da cewa an kwace bindigoginsu na aiki.
Sai dai, daga baya an gano babur din da jami’an tsaron suka yi amfani da shi.
An fara neman maharan
Bayan harin, jami’an tsaro sun kaddamar da bincike a kauyukan da ke kewaye domin gano maharan tare da kwato bindigogin da suka sace.
A lokacin wallafa wannan rahoto, ba a tabbatar da sunayen jami’an tsaron da aka kashe a hukumance ba.
Haka kuma, kokarin samun karin bayani daga kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Plateau, SP Alfred Alabo, da jami’in yada labarai na Operation Enduring Peace, Kyaftin Chinonso Polycarp Oteh, bai yi nasara ba.
Karanta wasu karin labaran kan 'yan bindiga
- Mutanen da ke tserewa 'yan bindiga sun nutse a cikin kogi a Sokoto
- Hankula sun tashi da 'yan bindiga suka nemi N80m bayan sace basarake
- Hankula sun tashi da 'yan bindiga suka babbake mutane a wani sabon harin ta'addanci
- 'Yan bindiga sun kwashi kashinsu a hannu da suka fafata da 'yan bindiga a Sokoto

Source: Facebook
'Yan bindiga sun sace basarake
A wani labarin kuma, kun ji cewa yan bindiga sun sace dagacin ƙauyen Patiko, Mallam Haruna Abubakar, a gundumar Zugurma da ke karamar hukumar Mashegu a jihar Neja.
Wani mazaunin yankin mai suna Aliyu Usman ya bayyana cewa ‘yan bindigar sun mamaye ƙauyen ne da tsakar daren ranar Juma’a, 31 ga watan Yulin 2026.
Maharan wadanda suke dauke da makamai sun riƙa harbe-harbe ba gaira ba dalili tare da kewaye gidan hakimin kafin su tafi da shi.
Asali: Legit.ng
