Gwamna Ya Yanke Hukunci, Ya Yi Wa Shugaba Tinubu Alkawarin 95% na Kuri'u a Zaben 2027

Gwamna Ya Yanke Hukunci, Ya Yi Wa Shugaba Tinubu Alkawarin 95% na Kuri'u a Zaben 2027

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

  • Gwamna Uba Sani ya sha alwashin bai wa Shugaba Bola Tinubu akalla kashi 95% na kuri'un mutanen Kaduna a zaben 2027
  • Gwamnan ya yabawa Tinubu kan ayyukan raya kasa da ake aiwatarwa a Arewacin Najeriya, yana mai cewa an riga an kammala zabe mai zuwa
  • Malam Uba Sani ya ce babu wani shugaban Najeriya da ya yi wa Arewa ayyukan ci gaba kamar Tinubu

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Kaduna, Nigeria - Gwamnan Kaduna, Sanata Uba Sani, ya bayyana kwarin gwiwar cewa Shugaba Bola Ahmed Tinubu zai samu gagarumar nasara a jihar a zaben shekarar 2027.

Gwamnan ya yi wannan bayani ne ranar Talata yayin kaddamar da aikin gina titin Kaduna zuwa Birnin Gwari mai tsawon kilomita 122.

Uba Sani.
Gwamnan Kaduna, Malam Uba Sani yana jawabi a taron tabbatar da goyon baya ga Shugaba Bola Tinubu Hoto: Uba Sani
Source: Facebook

A rahoton Vangaurd, Uba Sani ya kuma yabawa shugaban kasa kan abin da ya bayyana a matsayin gagarumin zuba jari a Arewacin Najeriya.

Kara karanta wannan

Tsohuwar gaba ta dawo, Wike ya faɗi yadda Rotimi Amarchi ya lalace

"Kaduna ita ce zuciyar Arewa"

Uba Sani ya ce jihar Kaduna na da muhimmanci ta fuskar siyasa da tattalin arziki a Arewacin Najeriya, yana mai cewa ci gaban jihar na amfani ne ga daukacin yankin.

Ya ce:

"Ina tabbatar muku Kaduna ita ce babban birnin Arewacin Najeriya. Kowa yana alfahari da Kaduna. Ci gaban Kaduna ci gaba ne ga dukkan jihohin Arewa, ko muna so ko ba ma so."

Ya yi alkawarin marawa Tinubu baya

Gwamnan ya gode wa Shugaba Tinubu bisa fahimtar muhimmancin Kaduna, tare da tabbatar da cewa gwamnatin jihar za ta ci gaba da ba shi cikakken goyon baya.

Uba Sani Y'ya ce:

"Za mu ci gaba da nuna goyon bayanmu. Za mu ci gaba da marawa shugaban kasa baya."

An ware wa Tinubu 95% na kuri'un Kaduna

Uba Sani ya ce yana da yakinin cewa Tinubu zai samu akalla kashi 95 cikin 100 na kuri'un da za a kada a Kaduna.

Kara karanta wannan

Layi ya zo kan talakawa, gwamna zai raba Naira biliyan 4 a mazabun jiharsa

A cewarsa:

"Ba ni da wata shakka cewa an riga an kammala zaben 2027. Ba ni da wata shakka cewa za mu ba shugaban kasa akalla kashi 95 cikin 100 na kuri'un Kaduna. Duk wanda bai yarda ba, ina shirye ya kalubalance ni."
Uba Sani.
Gwamna Uba Sani lokacin da ya kai ziyara ga Shugaba Bola Ahmed Tinubu a fadarsa da ke Abuja Hoto: Uba Sani
Source: Twitter

Ya yabawa Tinubu kan ayyukan Arewa

Gwamnan ya sake nanata matsayinsa na baya cewa babu wani shugaban Najeriya da ya aiwatar da ayyukan ci gaba a Arewacin kasar kamar Shugaba Tinubu.

Ya ce kimanin watanni biyu da suka gabata ya bayyana hakan a fili, kuma har yanzu babu wanda ya gabatar da hujjar da ta saba da wannan ikirari.

Ya kara da cewa ayyukan da ake gudanarwa a sassa daban-daban na Arewa sun nuna irin kudirin shugaban kasa na bunkasa yankin, kamar yadda Leadership ta rahoto.

Uba Sani ya zabi mataimaki kirista

A wani labarin, kun ji cewa Gwamna Uba Sani ya bayyana Kirista, Jerry Adams, a matsayin mataimakinsa a zaben gwamnan Kaduna na 2027.

Gwamnan ya bayyana hakan ne a wata sanarwa da ya fitar, inda ya ce ya dauki matakin ne bayan gudanar da tuntuba da dama, nazari mai zurfi da kuma addu'o'i.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262