Arewa
Wasu 'yan bindiga sun kai farmaki fadar Sarkin Zurmi a jihar Zamfara inda suka hallaka mutane uku yayin da suka lalata karfunan sabis a yankin yayin farmakin.
Mazauna kauyen Allawa da ke karamar hukumar Shiroro a jihar Neja sun shiga fargaba bayan sojoji sun tattare kayansu a kauyen sun fice da safiyar yau Alhamis.
Daruruwan matasa sun mamaye sakatariyar APC a birnin Tarayya Abuja inda suke neman shugaban jam'iyyar, Abdullahi Umar Ganduje ya yi murabus daga mukaminsa.
Hukumar EFCC ta sanar da janye daukaka kara da ta yi kan hukuncin kotu da ta dakatar da ita yunkurin cafke tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello.
Yayin da aka kafa kwamitin binciken tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, Majalisar jihar ta tura takarda ga kwamishinan kudi kan kaddamar da binciken.
Akalla kaso 62.6% na kananan yara a jihar Yobe aka tursasasu suke yin aikatau. Wannan ya sa jihar ta fi ko ina yawan yara masu aikin bauta a Arewacin Najeriya.
Tsohon Sarkin Damaturu na farko, Alhaji Mai Aliyu Muhammad Biriri ya riga mu gidan gaskiya a kasar Saudiyya ya na da shekaru 82 a duniya bayan fama da jinya.
Masu ruwa da tsakin APC a shiyyar Arewa ta Tsakiya sun fara neman a dawo da kujerar shugaban jam'iyyar APC na kasa zuwa yankinsu, sun yarda a dakatar da Ganduje.
Shugaba hukumar yaki da cin hanci a jihar Kano, Muhyi Magaji Rimingado ya bayyana yadda suka gano yadda tsohon gwamnan jihar, Abdullahi Ganduje ya yi badakala.
Arewa
Samu kari