Latest
Tsohon Sufeto Janar na ‘yan sanda a Najeriya, Usman Alkali Baba, ya shiga takarar gwamnan Yobe bayan yarjejeniyar tsayar da ɗan takara guda ta rushe.
Peter Obi ya tabbatar da ficewarsa daga ADC sakamakon rikicin cikin gida, inda ya jaddada cewa har yanzu yana da yakinin samar da sabuwar Najeriya.
Jam'iyyar ADC mai adawa a Najeriya ta fitar da jadawalin lokacin gudanar da zaben fidda gwani. Ta bayyana kudaden fom na masu neman takara a inuwarta.
Mai neman takarar kujerar sanatan Kebbi ta Tsakiya karkashin inuwar jam'iyyar APC, Kabiru Sani Giant, ya yi watsi da batun sulhu. Ya ce mutane na son canji.
Gwamnan jihar Sokoto, Ahmad Aliyu, ya yi tsokaci kan batun tattaunawa da 'yan bindiga. Ya bayyana cewa gwamnonin Arewa maso Yamma ba su tattauna da 'yan bindiga ba.
Gwamnan jihar Katsina, Dikko Radda ya nuna alhini kan rasuwar fitaccen mawakin gargajiyar Hausa, Alhaji Surajo Mai-Asharalle, wanda ya rasu bayan fama da jinya.
Tsohon ministan makamashi, Adebayo Adelabu ya bayyana cewa Bola Tinubu ya ba shi izinin barin mukaminsa domin fara shirye-shiryen neman kujerar gwamnan Oyo.
Farfesa Isa Pantami ya dakatar da mataimakinsa na kafafen sada zumunta sakamakon kiran abokan hamayya da "munafukai" a wani sako da aka wallafa ba da izininsa ba.
Shugaban kasar Amurka, Donald Trump, ya yi tsokaci kan sharuddan da Iran ta mika domin kawo karshen yaki. Trump ya ce Amurka na nazari kan sharuddan.
Masu zafi
Samu kari