Ministan Tinubu Ya Tayar da Rigima kan Hana Shi Takarar Gwamna, Ya Soki APC

Ministan Tinubu Ya Tayar da Rigima kan Hana Shi Takarar Gwamna, Ya Soki APC

  • Tsohon ministan makamashi a Najeriya, Adebayo Adelabu ya yi martani bayan rahoton cewa APC ta tsayar da dan takara a Oyo
  • Adelabu ya ƙaryata rahoton cewa an tsayar da Sharafadeen Alli a matsayin ɗan takarar gwamna a Oyo domin zaɓen 2027
  • Tsohon ministan ya bayyana cewa Bola Tinubu ya ba shi izinin barin mukaminsa domin fara shirye-shiryen neman kujerar gwamnan Oyo

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Ibadan, Oyo - Tsohon ministan makamashi, Adebayo Adelabu, ya yi watsi da matakin API kan dan takarar gwamna a Oyo.

Adelabu ya karyata cewa jam'iyyar da shugabannin APC amince da Sanata Sharafadeen Alli a matsayin ɗan takarar gwamnan Oyo na bai ɗaya.

Ministan Tinubu ka iya rasa tikitin takarar Gwamna
Tsohon ministan makamashi, Adebayo Adelabu da Bola Tinubu. Hoto: Bayo Adelabu, Bayo Onanuga.
Source: Facebook

A ranar Juma’a ne wasu jiga-jigan APC a Oyo suka bayyana goyon bayansu ga Alli yayin wani taro da aka gudanar a Ibadan domin shirya zaɓen 2027, cewar TheCable.

Kara karanta wannan

'Ba sulhu a Nasarawa' Tsohon IGP ya rusa shirin APC, ya turje kan takarar gwamna

Adelabu ya yi murabus saboda takara

Tsohon minista, Adebayo Adelabu ya yi murabus daga mukaminsa na ministan harkokin makamashi domin neman takarar gwamna a jihar Oyo.

Adelabu ya mika takardar ajiye aikinsa a hukumance ga sakataren gwamnatin tarayya, George Akume, yau Laraba, 22 ga watan Afrilu, 2026.

Ya ba da shawarar kirkiro mukamin Ministan Makamashi mai kula da dukkan fannoni domin hada kai wajen gyaran bangaren wuta, gas da sauran fannoni.

Tsohon minista ya fusata bayan hana shi takarar gwamna
Tsohon ministan makamashi, Adebayo Adelabu. Hoto: Bayo Adelabu.
Source: Facebook

Takarar Gwamna: Adelabu ya soki APC

Tsohon sanata Ayo Adeseun ya ce shugaban ƙasa Bola Tinubu ya nuna goyon baya ga takarar Sharafadeen Alli, yana mai cewa ra’ayin shugaban ya kamata ya samu kulawa.

Sai dai Adelabu ya bayyana cewa kafin ya yi murabus daga matsayin ministan lantarki, ya nemi ganawa kai tsaye da Tinubu domin tattauna burinsa na takarar gwamna.

Yayin wani taron APC a Ibadan da Kudu maso Gabas, Adelabu ya ce shugaban ƙasa ya ba shi damar sauka daga mukami domin fara shirye-shiryen siyasa a Oyo.

Kara karanta wannan

APC ta fitar da dan takarar gwamna a Oyo, ta juyawa ministan Tinubu baya

'Yadda Tinubu ke goyon bayan Adelabu'

Adelabu ya bayyana cewa Tinubu ya shaida masa cewa ya daɗe yana son zama gwamna, kuma ba zai hana shi cika wannan buri ba, cewar Daily Post.

Ya ce shugaban ƙasar ya kuma bayyana yiwuwar cimma matsaya ta bai ɗaya tsakanin masu neman takara ko kuma gudanar da zaɓen fidda gwani kai tsaye.

Tsohon ministan ya ce duk wanda ke cewa shugaban ƙasa ya amince da wani ɗan takara daban yana ƙarya domin shugaban bai sanar da hakan ga kowa ba.

Adelabu ya ƙara da cewa idan har Tinubu zai goyi bayan wani ɗan takara a Oyo, to shi ne zai fi dacewa da wannan goyon baya.

Adelabu ya fadi dalilin murabus daga minista

Mun ba ku labarin cewa tsohon ministan wutar lantarki, Adebayo Adelabu ya musanta rahotanni da ake yadawa cewa ya yi murabus ba tare da izinin Bola Tinubu ba.

Daya daga cikin hadimansa, Femi Awogboro ya ce sai da Shugaba Bola Tinubu ya amince kuma ya sa albarka kafin Adelabu da ajiye aiki.

Ya jaddada cewa tsohon ministan zai maida hankali wajen neman takarar gwamnan Oyo a zaben 2027, domin ci gaba da hidimata wa al'umma.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.