Fitaccen Mawakin Gargajiya a Arewa, Mai Asharalle Ya Yi Bankwana da Duniya
- Gwamna Dikko Radda ya nuna alhini kan rasuwar fitaccen mawakin gargajiyar Hausa wanda ya rasu bayan fama da jinya a Katsina
- Marigayin ya bar mata uku da yara 22 tare da jikoki 46, yayin da gwamnati ta bayyana shi a matsayin ginshikin al’adun Hausawa
- Gwamna Radda ya ce Surajo Mai-Asharalle ya taka muhimmiyar rawa wajen bunkasa wakokin Asharalle da kiɗan farauta, inda aka san shi da Farautan Katsina
Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.
Katsina - Gwamnan Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, ya bayyana matukar alhini kan rasuwar shahararren mawakin gargajiyar a Arewa.
Majiyoyi sun ce Alhaji Surajo Mai-Asharalle, ya rasu ranar Alhamis, 30 ga Afrilu, 2026, bayan doguwar jinya a Asibitin Koyarwa na Tarayya da ke Katsina.

Source: Facebook
Legit Hausa ta samu wannan sanarwa ce daga shafin X na gwamnatin jihar Katsina wanda Kaulaha Mohammed ya sanya wa hannu.
Suraji Mai Asharalle: Gwamna Radda ya yi ta'aziyya
Marigayin ya rasu ya bar mata uku da yara 22 tare da jikoki 46, Gwamna Radda ya bayyana marigayin a matsayin babban gwarzon al’adu.
An ce marigayin ya sadaukar da rayuwarsa wajen karewa da bunkasa wakokin gargajiyar Hausa wanda ya kara inganta al'adar ƙasar Hausa da kuma kara zaman lafiya a yankin.
Ya ce Surajo Mai-Asharalle ya yi fice tun daga shekarun 1990 saboda salon wakokinsa na Asharalle da kuma jagoranci a bangaren kiɗan farauta, abin da ya sa aka ba shi lakabin Farautan Katsina.
Gwamna Radda ya kara da cewa marigayin almajirin fitaccen mawaki Dakta Mamman Shata ne, wanda ya taba karrama shi da sarautar Garkuwan Mawaƙa saboda gudunmawar da ya bayar ga harkar waka.
Sanarwar ta ce:
“Alhaji Surajo ya kasance mai kare al’adunmu wanda wakokinsa suka taimaka wajen adana tarihi da kuma zaburar da al’umma daban-daban."

Source: Twitter
'Rashin da Katsina da Hausawa suka yi'
Gwamna Radda ya bayyana rasuwar mawakin a matsayin babban rashi ga Katsina da daukacin al’ummar Hausawa, yana mai cewa an rasa mutum mai daraja da kuma wata alama ta asalin al’adu.
A madadin gwamnati da al’ummar Katsina, gwamnan ya mika sakon ta’aziyya ga iyalan marigayin da masu harkar waka, tare da addu’ar Allah ya jikansa da rahama.
Gwamnan ya ba iyalan marigayin hakuri juye wannan babban rashi da suka yi duba da irin gudunmawa da ya bayar da a'adun Hausawa inda ya yi masa addu'ar samun rahama a gobe kiyama.
An nada ɗan Gwamna Dikko Radda sarauta
A wani labarin, an ji cewa mai martaba Sarkin Katsina, Abdulmumini Kabir Usman, ya jagoranci nadin sarautar dan Gwamna Dikko Umaru Radda a jihar.
Taron naɗin sarautun ya samu halartar gwamnoni, sarakuna da manyan baƙi daga sassan Najeriya da kuma jamhuriyar Nijar makwabciya.
Sarkin Katsina ya yi kira ga jama’a su rungumi zaman lafiya, haɗin kai da kyawawan ɗabi’u domin tabbatar da ci gaba da zaman lafiya a al’umma
Asali: Legit.ng

