An Yi wa Nafiu Bala Barazanar Raba Shi da Rayuwarsa kan ADC? Gaskiya Ta Fito
- Shugaban tsagin ADC a Najeriya, Nafi’u Bala ya yi magana game da barazanar da aka ce an yi masa kan jam'iyyar adawa
- Nafiu Bala ya musanta rahoton da ke cewa ya yi nadamar rikicin jam’iyya tare da zargin rayuwarsa na cikin haɗari
- Ya bayyana rahoton a matsayin ƙarya da farfaganda, yana mai cewa bai ba da wata hira ba kuma bai tura kowa ya yi magana madadinsa ba
Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.
Gombe - Shugaban tsagin jam’iyyar ADC, Nafi’u Bala, ya yi martani game da rahoton cewa an yi masa barazana.
Matashin ya musanta wani rahoto da ya ce ya nuna nadama kan rawar da ya taka a rikicin cikin jam’iyyar.

Source: Facebook
Bala, wanda ya tsaya takarar gwamna a Gombe ƙarƙashin ADC a zaɓen 2023, ya ce rahoton da ke ikirarin rayuwarsa na cikin haɗari ƙarya ne, cewar Punch.
Rahoton ya ambato Bala yana cewa bai yi tsammanin rikicin siyasar cikin jam’iyyar zai kai wannan matsayi mai muni da ya gagari shawo kansa ba.
An kuma ruwaito shi yana cewa ya yi nadamar rawar da ya taka a rikicin ADC saboda lamarin ya kai matsayin da rayuwarsa ta shiga haɗari.
Sai dai a wata sanarwa da ya fitar ranar Lahadi, Bala ya bayyana rahoton a matsayin ƙarya, sharri da kuma yunƙurin bata masa suna a idon jama’a.
Ya jaddada cewa bai yi wata hira ba kan rikicin, kuma bai bai wa wani izinin yin magana a madadinsa dangane da lamarin ba.
Bala ya bayyana cewa duk matakan da ya ɗauka a jam’iyyar sun bi tsarin doka bayan tsohon shugaban ƙasa na ADC, Ralph Nwosu, ya yi murabus.
Ya ce duk wani zargi da ke nuna ya nuna nadama ko yana ƙoƙarin nesanta kansa daga rikicin shugabanci gaba ɗaya ƙarya ne marar tushe.

Source: Twitter
Shugaban tsagin ADC ɗin ya ce bai umurci wani mutum, har da wanda aka ambata a rahoton, ya yi magana a madadinsa kan rikicin ba.
Bala ya kuma musanta rahotannin da ke cewa rayuwarsa ko ta iyalansa na cikin barazana, yana cewa an kirkiri labarin ne domin tayar da tausayi.
Dangane da zargin da ya haɗa sunan Leke Abejide cikin rikicin, Bala ya ce bai taɓa zargin ɗan majalisar da watsi ko cin amana ba.
Sai dai ya amince cewa ficewar Abejide daga ADC babban rashi ne ga jam’iyyar, yana mai yabawa gudummawar da ya bayar wajen bunƙasa jam’iyyar.
Bala ya sake jaddada cewa zai ci gaba da neman hakkinsa a kotu, yana mai cewa shari’ar na gaban Babbar Kotun Tarayya a yanzu.
Ya ce matsayinsa ba ya da alaƙa da wata riba ko diyya ta siyasa, illa kare kundin tsarin mulkin ADC musamman sashe na 8(2) da 9(4).
A ƙarshe, Bala ya bayyana rahoton a matsayin farfagandar siyasa da aka shirya domin yaudarar jama’a da kuma tasiri kan shari’ar da ke kotu.
Asali: Legit.ng

