Jami’an Gwamnatin Trump 5 da Yakin Iran, Isra’ila Ya Jawo Suka Bar Kujerunsu
Shugaba Donald Trump ya rasa wasu manyan jami’an gwamnatinsa biyar tun bayan fara yakin Amurka da Isra’ila da Iran
Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.
Washington DC, US - Yayin da ake ci gaba da yaki tsakanin Iran da Isra'ila, wasu Amurkawa na nuna rashin amincewa kan rikicin.
Wasu ministoci sun bar Majalisar zartarwa a gwamnatin Donald Trump da shugabancin sojojin Amurka tun bayan fara yakin Iran.

Source: Facebook
Shugaba Donald Trump da Ministan tsaro Pete Hegseth sun jagoranci korar wasu ministoci da manyan shugabannin soja a watannin bazarar bana, cewar Washington Post.
Korarren sakataren rundunar ruwa John Phelan ya bar mukaminsa bayan watanni 13, yayin da gwamnatin Trump ke fuskantar rikice-rikice da ficewar manyan jami’ai.
Jami'an da suka bar gwamnatin Donald Trump
Tun daga watan Maris, 2026 akalla manyan jami’ai biyar aka tilasta masu sauka daga mukamansu ko suka yi murabus saboda matsin lamba daga gwamnati.

Kara karanta wannan
Iran ta yi magana, da yiwuwar yaki ya kuma barkewa tsakanin kasar Musulunci da Amurka
Wannan sauyi ya zo ne lokacin da yakin Amurka da Isra’ila da Iran ya jawo matsala, tashin farashin makamashi da faduwar karbuwar Trump.
Legit Hausa ta yi duba game da jerin jami’an da suka rasa kujerunsu a gwamnati da kuma dalilan ficewarsu.
1. Sakataren Rundunar Ruwa, John Phelan
John Phelan ya bar mukaminsa da ya dade yana rike da ita, kamar yadda ma’aikatar tsaro ta Pentagon ta sanar ana cikin yaki da Iran.
Mai magana da yawun Pete Hegseth mai suna Sean Parnell ya ce sakataren rundunar ruwa ya bar Pentagon bayan watanni 13 a aiki.
Wakilin Legit Hausa ya ruwaito cewa gwamnati ta ce an bukaci attajirin da ya tara kudin yakin neman zaben Trump ya sauka.
Majiyoyi biyar sun shaida cewa Phelan ya yi ta rikici da Hegseth kan yadda yake tafiyar da aikin gina jiragen ruwa.

Source: Twitter
2. Babban Hafsan Sojoji, Janar Randy George
Janar Randy George ya yi ritaya daga mukaminsa a wannan watan yayin da yakin Iran ke ci gaba da daukar hankali.
An yi hasashen zai ci gaba da zama har zuwa shekarar 2027, amma Pete Hegseth ya bukaci ya sauka daga mukaminsa.

Kara karanta wannan
Zambar N1.5bn: Gwamnatin Kano za ta hukunta jami'an da suka tsakure albashin ma'aikata
Jami’an tsaro sun bayyana cewa an kuma cire Janar David Hodne da Manjo Janar William Green Jr. daga mukamansu ba tare da bayyana dalili ba.
Ficewar George ya bai wa Hegseth damar sake tsara kwamitin hafsoshin soja da ke bai wa shugaban kasa da ministan tsaro shawara.

Source: Twitter
3. Babbar Lauyar Kasa, Pam Bondi
Pam Bondi ta bar mukaminta a wata Afrilun 2026 bayan watanni 14 tana jagorantar ma’aikatar shari’a ta Amurka.
Trump ya bayyana Bondi a matsayin “babbar mai kishin Amurka kuma aminiya,” yana cewa za ta koma wani muhimmin aiki a bangaren masu zaman kansu.
Rahotanni sun ce Trump ya nuna rashin jin dadi kan jinkirin Bondi wajen bin abokan hamayyarsa ta fuskar shari’a.
An maye gurbinta da Todd Blanche, tsohon lauyan Trump, har sai an tabbatar da sabon wanda zai karbi mukamin.
4. Ministar Kwadago, Lori Chavez-DeRemer
Ministar kwadago Lori Chavez-DeRemer ta yi murabus domin komawa aiki a bangaren masu zaman kansu kamar yadda Fadar White House ta sanar.
Murabus din ya biyo bayan matsin lamba daga zarge-zargen rashin da’a wajen tafiya da kudin gwamnati domin bukatun kai duk da wasu na danganta hakan da yakin Iran.

Kara karanta wannan
Amurka ta tafka asara a yaki da kasar Musulunci ta Iran, ta kashe kimanin Dala biliyan 25
Lauyanta Nick Oberheiden ya ce ta sauka ne domin kada binciken ya hana ma’aikatar kwadago gudanar da ayyukanta yadda ya kamata.
Mai magana da yawun White House Steven Cheung ya ce mataimakinta Keith Sonderling zai zama mukaddashin shugaban ma’aikatar.

Source: Getty Images
5. Ministar Tsaron Cikin Gida, Kristi Noem
Donald Trump ya sanar a watan Maris, 2026 cewa zai maye gurbin Kristi Noem da Sanata Markwayne Mullin a ma’aikatar tsaron cikin gida.
An mayar da ita wata sabuwar kujera mai suna “Jakadiyar Musamman ta Garkuwar Nahiyar Amurka” domin kula da tsaro a yankin yammacin duniya.
Sauyin ya biyo bayan suka masu yawa kan yadda take tafiyar da shirin korar bakin haure daga Amurka, cewar Al Jazeera.
Hatta wasu ‘yan jam’iyyar Republican sun nuna shakku kan dacewarta da mukamin da take rike da shi.
Babban hadiminta Corey Lewandowski, wanda ya taba aiki tare da Trump kafin a taba korarsa, shi ma ya bar ma’aikatar a watan guda.
Nukiliya: Mojtaba Khamenei ya caccaki Amurka
A baya, mun ba ku labarin cewa jagoran addin a Iran, Ayatollah Mojtaba Khamenei ya yi magana game da shirinta na nukiliya a kasar.
Khamenei ya ce Iran ba za ta mika shirinta na nukiliya da makamai masu linzami ba, duk da matsin lambar Amurka.
Ya zargi Amurka da tsoma baki a yankin Gulf, yana mai cewa Iran za ta ci gaba da kare muradunta duk rikicin da ake ciki.
Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.
Asali: Legit.ng
