Amurka Ta Lissafa Najeriya da Wasu Kasashen Afrika dake Fuskantar Barazanar Tsaro
- Amurka ta ce fataucin miyagun kwayoyi da safarar mutane sun karu fiye da sau shida a Afirka cikin shekaru biyu
- Najeriya na cikin kasashen da za su amfana da sabon shirin Amurka na bunkasa manyan ayyukan more rayuwa masu jawo masu zuba jari
- AFRICOM ta ce hadin gwiwa tsakanin kasashen Afirka ne kadai zai iya dakile sabbin barazanar tsaro
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Sani Hamza ƙwararren edita ne a fannin nishaɗi, al'amuran yau da kullum, da kuma siyasa, wanda ke da shekaru sama da takwas a aikin jarida
Gwamnatin Amurka ta yi gargadin cewa Najeriya da sauran kasashen Afirka na fuskantar karuwar barazanar tsaro fiye da sau shida cikin shekaru biyu da suka gabata, sakamakon karuwar safarar miyagun kwayoyi da kuma cinikin mutane a nahiyar.
Haka kuma, Amurka ta bayyana Najeriya, Kenya da Cote d'Ivoire a matsayin manyan kasashen da za su ci gajiyar sabon shirinta na taimakawa gwamnatocin Afirka wajen tsara manyan ayyukan more rayuwa da za su iya jawo jarin kamfanonin Amurka.

Source: Getty Images
AFRICOM ta bayyana sabbin barazanar tsaro
Daraktan sashen dabarun sufuri na rundunar AFRICOM ta Amurka, Birgediya Janar Paul G. Filcek, ne ya bayyana hakan yayin taron manema labarai ta yanar gizo da ya yi da 'yan jaridar Afirka a gefen taron ALCS2026 in ji rahoton Vanguard.
An gudanar da taron ne tare da Ma'aikatar Tsaron Habasha, inda wakilai daga kasashe 39 na Afirka da kamfanoni masu zaman kansu 27 suka halarta domin tattauna hanyoyin inganta tsaro da hadin gwiwa.
Filcek ya ce nahiyar Afirka na fuskantar sabbin kalubalen tsaro da suka hada da safarar mutane da kuma fataucin miyagun kwayoyi, wanda ya ce ya karu fiye da sau shida idan aka kwatanta da shekaru biyu da suka gabata.
Yadda za a shawo kan matsalolin
Ya ce shawo kan irin wadannan matsaloli na bukatar hadin gwiwa tsakanin kasashen Afirka, ingantaccen tsarin sadarwa da kuma damar jigilar jami'an tsaro, kayan aiki da kayayyaki cikin gaggawa zuwa wuraren da ake bukata.
A cewarsa, wannan ne karo na farko da aka hada batutuwan dabarun sufuri da sadarwa cikin taro guda, yana mai cewa hakan zai kara karfin kasashen Afirka wajen tinkarar matsalolin tsaro na zamani.
Najeriya ta shiga shirin jawo jarin Amurka
A nasa bangaren, Mataimakin Sakataren Kasuwancin Amurka mai kula da Gabas ta Tsakiya da Afirka, Mark Mitchell, ya bayyana cewa Ma'aikatar Kasuwanci da Ma'aikatar Harkokin Wajen Amurka na gudanar da wani sabon shiri mai suna TABI.
Ya ce manufar shirin ita ce taimaka wa gwamnatocin Afirka wajen tsara manyan ayyukan more rayuwa da za su kasance masu jan hankalin masu zuba jari daga Amurka tare da samar da amfani ga al'ummomin kasashen.

Source: Twitter
Mitchell ya bayyana cewa Najeriya, Kenya da Cote d'Ivoire na daga cikin kasashen da Amurka ke aiki tare da su wajen inganta yanayin kasuwanci, tsarin gudanar da bayanai da kuma hada-hadar zuba jari.
Jaridar Tribune ta rahoto ya ce manufar shirin ita ce bai wa kasashen Afirka damar cin gashin kansu ta fuskar ci gaba, maimakon dogaro da tallafi daga kasashen waje.
Mitchell ya kara da cewa hadin gwiwar da Amurka ke yi da Najeriya da sauran kasashen ya nuna kudurinta na samar da kasuwanni masu gaskiya, gasa da kuma dokoki da ke kare ikon kasashe tare da inganta kirkire-kirkire da ci gaban tattalin arziki.
Zarrar sojojin Najeriya a Afrika
A wani labarin, mun ruwaito cewa, rundunar Sojin Najeriya ta samu lambar yabo daga African Security Watch a matsayin mafi ƙwarewa a Afirka wajen yaƙi da ta'addanci a 2025.
Shugaban Hafsan Sojin Ƙasa, Laftanar Janar Waidi Shaibu, ya sadaukar da lambar yabon ga sojojin da suka rasa rayukansu da iyalansu.
Kungiyar African Security Watch ta ce nasarorin rundunar sun samo asali ne daga haɗin gwiwa, tattara bayanan sirri da inganta horon sojoji
Asali: Legit.ng


