Minista a Gwamnatin Trump Ta Bar Mukaminta yayin da Yake Ci Gaba da Barazana ga Iran
- Gwamnatin kasar Amurka, karkashin jagorancin Shugaba Donald Trump, ta rasa daya daga cikin ministocinta
- Ministar kwadago, Lori Chavez-DeRemer, ta yi murabus daga mukaminta, inda za ta koma aiki a wani bangaren
- Tuni Daraktar yada labarai na fadar White House ta sanar da wanda zai ci gaba da rike ma'aikatar a matsayi na wucin gadi
Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi
Birnin Washington, Amurka - Ministar kwadagon Amurka, Lori Chavez-DeRemer, ta yi murabus daga Gwamnatin Donald Trump.
Ministar ta bar Gwamnatin Trump ne domin karbar aiki a kamfanoni masu zaman kansu, a daidai lokacin da ake gudanar da bincike na cikin gida kan zargin rashin da'a.

Source: Getty Images
Tashar Aljazeera ta kawo rahoton cewa daraktan sadarwa a fadar White House, Steven Cheung, ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa.
Ministar kwadago ta bar gwamnatin Trump
“Ministar kwadago Lori Chavez-DeRemer za ta bar gwamnati domin karbar wani matsayi a kamfanoni masu zaman kansu."
“Ta yi gagarumin aiki a mukaminta ta hanyar kare ma’aikatan Amurka, aiwatar da kyawawan ayyukan kwadago, da kuma taimakawa Amurkawa samun karin kwarewa don inganta rayuwarsu.”
- Steven Cheung
Steven Cheung ya kara da cewa Keith Sonderling ne zai yi aiki a matsayin ministan wucin gadi na ma’aikatar kwadago.
Lori Chavez-DeRemer ta yi godiya
A cikin wata sanarwa a shafinta na X, Chavez-DeRemer ta rubuta cewa:
"Abin farin ciki ne da alfahari a yi aiki a wannan gwamnati mai tarihi da kuma yi wa babban Shugaban kasa a rayuwata aiki.”
“Ina alfahari da cewa mun samu gagarumin ci gaba wajen ciyar da manufar Shugaba Trump gaba na dinke baraka tsakanin ‘yan kasuwa da 'yan kwadago da kuma sanya ma’aikatan Amurka a gaba a ko yaushe."
Akwai zarge-zarge a kan tsohuwar ministar
Tashar CNN ta ce gajeren wa’adin mulkin Chavez-DeRemer ya kasance cike da hargitsi yayin da take fuskantar bincike na cikin gida biyo bayan korafe-korafe a cikin ma’aikatar game da halayenta.

Kara karanta wannan
Saraki ya jefi gwamnatin Buhari da zargi kan fashin Offa, ya fallasa gwamnan Kwara
An taba bayar da rahoton cewa an haramta wa mijinta shiga babban ofishin ma’aikatar sakamakon zargin cin zarafin mata. An rufe binciken manyan laifuffuka kan wannan batu.

Source: Getty Images
A watan Maris, an tilasta wa biyu daga cikin manyan mataimakanta barin aiki a daidai lokacin da ake binciken rashin da'a a hukumar.
Tsawon watanni, ofishin babban sufeton ma’aikatar kwadago yana binciken wani korafi na cewa Chavez-DeRemer tana kwanciya da daya daga cikin jami’an tsaron dake kare ta.
Akwai sauran zarge-zargen halaye marasa dacewa, kamar tura ma’aikata su siyo mata giya da kuma kokarin amfani da tafiye-tafiyen aiki a matsayin uzurin tafiyar kashin kanta, kamar yadda wata majiya a ma’aikatar kwadago dake da masaniya kan lamarin ta bayyana.
Trump ya yi barazana ga Iran
A wani labarin kuma, kun ji cewa Shugaban kasar Amurka, Donald Trump, ya nuna kwarin gwiwar cimma yarjejeniya da Iran.
Donald Trump ya yi gargadin cewa idan hakan ba ta faru ba, ƙasar za ta fuskanci matsaloli masu tsanani fiye da duk abin da ta taɓa gani a baya.
Hakazalika, Trump ya yi gargaɗi mai tsauri kan batun makaman nukiliya, yana cewa bai kamata a bari Iran ta samu damar mallakar irin wannan makami ba.
Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.
Asali: Legit.ng
