Manyan Labarai A Yau
Hon. Mojisola Meranda ta karyata jita-jitar da ake yaɗawa a kafafen sada zumunta cewa ta yi murabus daga muƙaminta saboda wutar rikicin da ta ƙi cinyewa.
Kotun majistire mai zama a Ilorin, babban birnin jihar Kwara ta tasa keyar Abdulrahman Muhammed, wanda ya ce shi malamin musulunci ne zuwa gidan yari.
Kungiyar gwamnonin Najeriya watau NGF ta bayyana alhininta bisa rasuwar jagoran PANDEF, Edwin Clark da jagoran Afenifere, Ayo Adebanjo, ta ce kasa ta yi rashi.
Hukumar kididdiga ta kasa watau NBS ta bayyana cewa hauhawar farashin kayayyaki a Najeriya ya yi gagarumar faɗuwa daga 34% zuwa 24.48% a watan Janairu.
Wasu miyagu sun yi yunkurin kashe babban darkta a hukumar gidaje ta ƙasa watau FHA, Remi Omowaiye yayin da yake hanyar komawa Osogbo yau Litinin.
Ƴan Majalisa da ma'aikata sun ɓarke da zanga zanga a zauren majalisar dokokin jihar Legas, sun bayyana goyon bayansu ga Hon. Mojisola Meranda a zaman yau Litinin.
Dakarun rundunar sojojin sama na Najeriya sun jefa bam kan bayin Allah bisa kuskure a jihar Katsina. Mutane sun rasa rayukansu sakamakon jefa bam din.
Jami'an rundunar 'yan sandan Najeriya sun samu nasarar hallaka 'yan ta'adda a sassa daban-daban na kasar nan. 'Yan sandan sun kuma kwato makamai masu tarin yawa.
Jam'iyyar APC mai mulki a jihar Katsina ta lashe zaben shugabannin kananan hukumomin da aka gudanar a jihar. APC ta lashe dukkanin kujerun gabadaya.
Manyan Labarai A Yau
Samu kari