Kwankwaso Ya Yi wa APC Yasa a Kano, Manya a Jam'iyyar Sun Rungumi Kwankwasiyya

Kwankwaso Ya Yi wa APC Yasa a Kano, Manya a Jam'iyyar Sun Rungumi Kwankwasiyya

  • Mataimakin ɗan takarar shugaban ƙasa na NDC, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya karɓi wasu jiga-jigan APC da suka sauya sheka zuwa NDC a Kano
  • Tsohon kansilan mazabar Zango da wasu jiga-jigai a tafiyar APC mai mulki a yankinsu sun yanke kauna da zama a cikin jamiyyar a Kano
  • An gano irin tarbar da Kwankwaso ya yi masu yayin da ake harama na fara kamfen da tunkarar babban zaben 2027 a cikin tan watanni masu zuwa

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa.

Jihar Kano – Ɗan takarar mataimakin shugaban ƙasa na jam’iyyar NDC, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya kara rage wa APC mutane a jihar Kano.

Sanata Kwankwaso ya karɓi wasu mambobin jam’iyyar APC da suka sauya sheka zuwa NDC a Kano daga mazabar Zango inda suka karbi shahadar Kwankwasiyya.

Kara karanta wannan

'Ba jira': Kwankwaso ya fadi tanadin NDC wajen nada mukamai idan an zabe ta

Kwankwaso ya karbi sababbin yan jam'iyya
Sanata Rabiu Musa Kwankwaso tare da yan APC da suka sauya sheka Hoto; Hon Saifullahi Hassan
Source: Facebook

Hadimin dan takarar shugaban kasa, Hon. Saifullahi Hassan ne ya bayyana hakan a wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na X a ranar Litinin, 17 ga Agusta, 2026.

Kwankwas ya tarbi yan APC

A cikin sakon, Saifullahi Hassan ya ce daga cikin waɗanda suka sauya sheka akwai Hon. Nasiru Labaran Zage, tsohon kansilan Zango da ke ƙaramar hukumar Birni.

Haka kuma akwai daya daga cikin manyan APC a yankin, Alhaji Saminu Jibrin, tare da wasu mambobin APC daga suka yanke kauna da ci gaba da zama a jam'iyyarsu.

A cewar Saidullahi Hassan, an karɓi sabbin ’yan jam’iyyar a hukumance zuwa cikin NDC, inda aka kuma yi masu ado da jajayen hular Kwankwasiyya, wadda ta zama alamar magoya bayan Kwankwaso.

Jama'a sun yi maraba da sauya sheka

Sauyin shekar ya jawo martani daga wasu masu goyon bayan Kwankwasiyya a kafafen sada zumunta, inda suka bayyana farin cikinsu tare da yi wa sabbin mambobin fatan nasara.

Kara karanta wannan

'Ba su da sauran mamora a siyasa': Kwankwaso ya ce ta karewa su Ganduje a Kano

Sanata Kwankwaso ya yi maraba da yan APC
Yadda Kwankwaso ya yi wa dan APC da ya sauya sheka ado da jar hula Hoto: Hon Saifullahi Hassan
Source: Facebook

Bashir Nasir Labaran ya bayyana farin cikinsa, inda ya rubuta:

“Masha Allah. Na ji dadin hakan sosai. Allah ya kara maka lafiya mahaifina tare da Jagora.”

Shi ma Aminu AbdulRazaq Ali ya ce:

“Kwankwasiyya Amana. Allah yabamu nasara.”

Wani Young Alhaji ya wallafa cewa:

“Ma Sha Allah. Oga dai yana ta kwashe su Jagora."

Sauyin shekar na zuwa ne yayin da jam’iyyun siyasa ke ƙara ƙoƙarin faɗaɗa tasirinsu da samun sabbin mambobi a shirye-shiryen tunkarar zaɓukan da ke tafe.

Yaron Ganduje ya bar Kwankwaso

A baya, kun ji cewa yaron tsohon gwamnan jihar Kano, ‎Abdulaziz Abdullahi Ganduje ya koma jam’iyyar APC wanda dama daga cikin ta ya fito ba da dadewa ba domin hadewa da Kwankwaso.

Shugabannin APC na mazabar Ganduje a karamar hukumar Dawakin Tofa a Kano sun karbe shi ranar Lahadi 16 ga watan Agusta 2026 bayan ya yanke shawarar rabuwa da abokin hamayyar mahaifinsa.

A watan Mayu Abdulaziz ya rungumi NDC duk da mahaifinsa ya rike har shugabancin APC a matakin kasa kuma ana takun saka tsakaninsu bayan rashin fahimta ta siyasa ta gifta a tsakaninsu.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Ahmad avatar

Aisha Ahmad (Hausa editor) Edita ce a sashen Hausa na legit.ng. Ta samu horon aikin jarida, musamman ta bangaren tace labarai a Premier Radio, da ICIR, da Express Radio. Ta shafe sama da shekaru goma tana aikin ɗaukar rahoto a jihar Kano. aisha.ahmad@corp.legit.ng