Manyan Labarai A Yau
An samu tashin wata mummunar gobara a ofishin hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) da ke jihar Sokoto. Gobarar ta lalata muhimman kayayyaki.
Jagoran kungiyar yarbawa watau Afenifere, Ayodele Ayobanjo ya mutu da safiyar yau Juma'a, 14 ga watan Fabrairu, 2025 a gidansa da ke Lekki a jihar Legas.
Mai martaba Ohinoyi na Ebiralanda ya koma kan karagar mulki da kotu ta ba da umarnin kowa ya tsaya a matsayinsa har sai kotun ɗaukaka kara ta yi hukuncin ƙarshe.
Mazauna garin Maru a jihar Zamfara sun fito kan tituna domin nuna adawarsu kan karuwar hare-haren 'yan bindiga. Sun bukaci hukumomi su dauki mataki.
Shugaban kwamitin kasafin kudi na majalisar wakilai, Abubakar Kabiru Abubakar Bichi ya yi bayani kan dalilin kara N700bn a kasafin kudin shekarar 2025.
Jami'an rundunar 'yan sandan jihar Katsina sun samu nasarar dakile wani harin 'yan bindiga. Jami'an tsaron sun ragargaji 'yan bindigan tare da ceto mutane.
Wasu 'yan bindiga dauke da makamai sun kai hare-haren ta'addanci a jihar Kaduna. 'Yan bindigan sun yi awon gaba da mutane masu yawa tare da kona gidaje.
Dan majalisar wakilan Najeriya daga jihar Borno, Honorabul Ahmed Jaha, ya ce akwai gyararrakin da ya kamata a yi wa kudirin gyaran haraji da ke gaban majalisa.
Dakarun sojojin Najeriya masu aikin samar da zaman lafiya sun samu nasarori kan 'yan ta'adda a jihohin Zamfara da Sokoto. Sojojin sun hallaka kwamandoji masu yawa.
Manyan Labarai A Yau
Samu kari