Jihar Kano
Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf ya yi mutanen Kano da ke zaune a ciki da wajen ƙasar nan murnar dhiga sabuwar shekara tare da fatan samun saukin rayuwa.
Rundunar 'yan sandan jihar Kano ta fitar da rahoto kan nasarorin da ta samu a 2024, ta kama 'yan daba, 'yan fashi da masu garkuwa da mutane da karin mutane 2,425
Hukumar Hisbah ta cafke yara akalla 220 da ke gararamba a titunan jihar, inda aka gano sun fito daga jihohi akalla 14, daga ciki har da jamhuriyar Nijar.
Zainab Ado-Bayero ta yi barazanar kawo karshen rayuwarta sakamakon wahalar rayuwa da rashin tallafi tun bayan rasuwar mahaifinta, tsohon sarkin Kano.
Gwamna Abba Kabir Yusufna jihar Kano ta karawa shugaban ma'aikatan gwamnati, manyan sakatarori da wasu ma'aikata wa'adin shekara biyu a bakin aiki.
Kungiyar ACT ta bukaci gwamnatin Bola Ahmed Tinubu da ta gaggauta yin bincike a kan dalilan jam'an tsaro na kai hare-hare kan fararen hula a sassan Arewa.
Sanusi II ya bukaci kasashen Yamma su zuba jari a Arewa ta hanyar gina makarantu, asibitoci da masana’antu, maimakon yin wa'azin da zai jawo kiyayya tsakanin addinai
Yayin da ake ta ce-ce-ku-ce kan kudirin haraji, Dan Majalisar NNPP daga Kano, Dr Mustapha Ghali, ya ce Najeriya ba ta shirya don aiwatar da dokar gyaran haraji ba.
Dan majalisar Kano, Dr. Mustapha Ghali ya ce bai dace takwarorinsa daga Arewa su zuba idanun a kan kudirin harajin da gwamnatin Bola Ahmed Tinubu ta gabatar masu ba.
Jihar Kano
Samu kari