Sarautar Kano: Babban Malami Ya Hango Matsala, Ya Aika Muhimman Sako ga Sanusi II

Sarautar Kano: Babban Malami Ya Hango Matsala, Ya Aika Muhimman Sako ga Sanusi II

  • Fitaccen limamin coci, Primate Elijah Babatunde Ayodele, ya bayyana wahayin da aka ƙara masa kan wasu manyan mutane a Najeriya
  • Ayodele, wanda ya yi kaurin suna wajen hasashen abin da zai faru a nan gaba, ya taɓo batun sarkin Kano na 16, Muhammad Sanusi II
  • Jihar Kano ta faɗa a rikicin sarauta tun lokacin da Majalisar Dokoki ta rusa masarautun biyar, Gwamna Abba Kabir kuma ya dawo da Sanusi II

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Kano - Yayin da ake ci gaba da rigimar sarautar Kano, fitaccen limamin cocin nan, Primate Elijah Ayodele ya ja kunnen sarki na 16, Muhammasu Sanusi II.

Primate Ayodele, shugaban cocin INRI Evangelical Spiritual Church ya buƙaci Muhammasu Sanusi II ya yi taka tsan-tsan kuma ya bi a hankali.

Primate Ayodele.
Primate Ayodele ya gargaɗi Muhammadu Sanusi II Hoto: Primate Babatunde Elijah Ayodele, Adeyanju Deji
Asali: Facebook

Limamin cocin ya yi wannan gargaɗi ne a wata sabuwar hira da aka yi da shi wacce jaridar Tribune Nigeria ta wallafa.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Babban malamin ya bukaci Muhammadu Sanusi II da ya yi taka-tsantsan, "musamman game abin da yake sha."

Kano: Primate Ayodele ya gargadi Sanusi II

Ayodele ya ce:

"Sarki (Sanusi Lamido), Sanusi, dole ne ya yi hankali, musamman game da abin da yake sha.”

Idan ba ku manta ba, a ranar 23 ga Mayu, 2024, Gwamna Abba Kabir Yusuf na Kano ya ba da umarnin tube Sarkin Kano na 15, Aminu Ado Bayero, tare da dawo da Sanusi Lamido Sanusi a matsayin sarki.

Gwamnan ya ɗauki wannan mataki ne bayan rattaɓa hannu kan dokar da ta rusa masarautu biyar da tsohon gwamnan jihar kuma shugaban APC na yanzu, Abdullahi Ganduje ya kirkiro.

Yadda rikicin sarauta ya ɓarke a Kano

Wannan lamari dai haifar rikici tsakanin ɓangarorin biyu, Aminu Ado Bayero da Muhammadu Sanusi II, kowane na bayyana kansa a matsayin sarki.

Sabuwar dokar da Gwamna Abba ya sa hannu bayan amincewar Majalisar dokoki Kano ta soke dokar masarautu ta 2019, wadda ta tsinka masarautar Kano zuwa guda biyar.

A ranar da mai girma gwamnan ya soke dokar, ya sanar da dawo da Sanusi II kan karagar sarauta.

A halin yanzu, sarkin da aka tube, Aminu Ado Bayero, yana kalubalantar tsige shi a kotu, kuma yana zaune a fadar Nassarawa a cikin birnin Kano, bayan Sanusi ya karɓi babbar fadar masarauta.

Primate Ayodele.
Primate Ayodele ya ja kunnen Muhammadu Sanusi II kan abubuwan da yake sha Hoto: Primate Ayodele
Asali: Twitter

Ayodele ya aika saƙo ga Sanusi II

Sai dai tun farko wannan rikici zuwa yanzu shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ya ƙi tsoma baki kan batun sarautar Kano duk da kiraye-kirayen da aka yi na ya shiga tsakani.

Da yake tsokacin kan halin da Sanusi II ke ciki, Primate Ayodele ya gargaɗi basaraken ya yi taka tsan-tsan musamman da abubuwan da ake kawo masa na sha.

Sanusi II ya halarci taron Tijjaniyya

A wani labarin, kun ji cewa Mai Martaba Sarkin Kano na 16, Muhammad Sanusi II, ya halarci babban taron Darikar Tijjaniyya a kasar Burkina Faso.

Rahotanni sun tabbatar da cewa an yi nadin sabon Khalifan Tijjaniyya a ƙasar Burkina Faso a ranar Lahadi, 4 ga Mayu, 2025.

Sanusi II, wanda shi ne Khaliphan Tijjaniyya na Najeriya ya samu halartar wannan taron nadin bayan samun katin gayyata.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262