Tura Ta Kai Bango: Mutane Sun Yi Zanga Zanga, an Tare Babbar Hanyar Niger

Tura Ta Kai Bango: Mutane Sun Yi Zanga Zanga, an Tare Babbar Hanyar Niger

  • Wasu ’yan yankin Mokwa ta sa aka toshe babbar hanyar Mokwa-Bida, bayan zargin yawaitar garkuwa da mutane da ’yan bindiga ke yi
  • Masu zanga-zangar sun ce an sace mazauna 15 a baya-bayan nan, kuma jami’an tsaro ba su samu nasarar ceto su ba
  • Toshe hanyar ya jefa matafiya cikin wahala, inda wasu suka shafe sama da sa’o’i biyar a Mokwa suna jiran gwamnatin ta kawo mafita

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Mokwa, Niger - Matafiya da masu amfani da babbar hanyar Mokwa-Bida a Niger sun shiga mawuyacin hali da ake ciki a yankin.

Rahotanni sun masu zanga-zanga sun toshe hanyar saboda zargin yawaitar hare-haren ’yan bindiga.

Ana zanga-zangaa Niger kan harin yan bindiga
Hanyar Mokwa zuwa Bida da ke jihar Niger da mutane suka toshe saboda hare-haren yan bindiga. Hoto: NAN.
Source: UGC

Wani wakilin Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya (NAN) da ya isa wurin ya ruwaito cewa masu zanga-zangar sun toshe dukkan hanyoyin shiga garin Mokwa.

Kara karanta wannan

Da gaske yan bindiga sun hallaka ciyaman da suka sace a Zamfara? An samu bayani

Muhimmancin da hanyar ke da shi

Babbar hanyar Mokwa-Bida muhimmiyar hanyar tarayya ce mai tsawon sama da kilomita 100, wadda ke haɗa masu ababen hawa daga Kudu maso Yamma zuwa Arewacin Najeriya.

Bayanan da aka tattara sun nuna cewa matafiya da dama sun makale a wurin tun daren Asabar, saboda rashin damar wucewa ta hanyar.

Ɗaya daga cikin masu zanga-zangar, Saliu Mohammed, ya yi zargin cewa wasu ’yan bindiga da ake zargi sun sace mazauna 15 na yankin a baya-bayan nan.

Mohammed ya kuma yi zargin cewa jami’an tsaro ba su samu damar ceto mutanen da aka yi garkuwa da su ba.

Ya ce masu zanga-zangar za su ci gaba da toshe hanyar har sai an ceto mutanen da aka sace.

Mutane sun fusata, sun toshe muhimmiyar hanya a Niger kan hare-haren yan bindiga
Taswirar jihar Niger da ke Tsakiyar Najeriya. Hoto: Legit.
Source: Original

Abin da matafiya ke cewa kan lamarin

Wata matafiya mai suna Joy Amaechi, wadda ke tafiya daga Ilorin zuwa Abuja, ta bayyana irin wahalar da ta fuskanta sakamakon toshewar hanyar.

Kara karanta wannan

Matsalar tsaro: An rufe makarantu 65 a Sokoto, Katsina da wasu jihohin Arewa

Amaechi ta ce ta shafe kusan sa’o’i biyar a Mokwa ba tare da samun mafita ba, inda ta yi kira ga gwamnati ta gaggauta shiga tsakani.

Wani direban kamfanin sufuri na jama’a, Henry Nwachuckwu, ya ce ya isa Mokwa da misalin ƙarfe 7 na safe ranar Lahadi, cewar Punch.

Ya bayyana cewa har zuwa lokacin da aka tattara rahoton, da misalin ƙarfe 10:30 na safe, masu zanga-zangar ba su bar babbar hanyar ba.

Toshewar hanyar ta haifar da cunkoso da tsaiko ga matafiya da direbobi, lamarin da ya ƙara tsananta wahalar da jama’a ke fuskanta sakamakon matsalar tsaro.

Masu zanga-zangar sun buƙaci hukumomin gwamnati da jami’an tsaro su gaggauta ɗaukar mataki domin ceto mutanen da ake zargin an sace tare da tabbatar da tsaron yankin.

Hanyar Mokwa-Bida na da matuƙar muhimmanci ga zirga-zirgar jama’a da jigilar kayayyaki tsakanin sassan Kudancin Najeriya da Arewa.

Rashin tsaro: An toshe hanya a Abuja

Kun ji cewa masu zanga-zanga sun toshe gadar Karu-Nyanya, sun bukaci gwamnati ta dauki mataki kan yawaitar hare-haren yan ta'adda a kasar nan.

Kara karanta wannan

Siyasa ta yi zafi, an bindige yaro ɗan shekara 12 yayin kamfen APC

Hakan dai na zuwa ne yayin da zanga-zangar adawa da matsalar rashin tsaro ta shiga rana ta uku a babban birnin tarayya Abuja.

Sha'anin tsaro na ci gaba da kara kamari a Najeriya musamman bayan sace dalibai da malamai a makarantu a jihohin Oyo da Borno.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.