Zaben 2027: ADC Ta Fitar da Jerin Sunayen 'Yan Takararta na Gwamna a Jihohi 28

Zaben 2027: ADC Ta Fitar da Jerin Sunayen 'Yan Takararta na Gwamna a Jihohi 28

  • ADC ta fitar da sunayen ’yan takarar gwamna da mataimakansu a jihohi 28 domin wakiltar jam’iyyar a zaɓen 2027
  • Daga cikin fitattun ’yan takarar akwai Halliru Dauda Jika a Bauchi, Herman Hembe a Benue da Zakari Mohammed a Kwara
  • A Kaduna, Isa Mohammed Ashiru zai tsaya takarar gwamna, yayin da Gbadebo Rhodes-Vivour zai fafata a Lagos ƙarƙashin tutar ADC

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

​​​​​​​​​​​​​​Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi

FCT, Abuja - Jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ta fitar da sunayen ’yan takararta na gwamna da mataimakansu da za su fafata a zaɓen 2027.

Mai magana da yawun jam’iyyar ADC, Bolaji Abdullahi, ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Juma’a, 4 ga watan Satumban 2026.

ADC ta fitar da 'yan takarar gwamna a jihohi 28
Kakakin ADC na kasa, Bolaji Abdullahi Hoto: @BolajiADC
Source: Facebook

Bolaji Abdullahi ya fitar da sanarwar ne a shafinsa na X dauke da sunayen 'yan takarar gwamnan na ADC.

Kara karanta wannan

'Yan Boko Haram sun yi wa motocin dan takarar gwamnan APC kwanton bauna a Borno

Ya ce jerin sunayen ya ƙunshi ’yan takarar gwamna da za su ɗauki tutar ADC a jihohi 28 na Najeriya.

Bolaji ya ce mutanen da aka zaɓa sun haɗa da maza da mata da za su wakilci manufofin jam’iyyar da kuma ƙudurinta na samar wa ’yan Najeriya shugabanci nagari da kuma wata sahihiyar mafita ta siyasa.

Fitattun ’yan takarar ADC

Daga cikin fitattun ’yan takarar da jam’iyyar ta bayyana akwai Sanata Halliru Dauda Jika a jihar Bauchi.

Haka kuma, tsohon ɗan Majalisar Wakilai, Herman Iorwase Hembe, zai tsaya takarar gwamna a Benue, yayin da tsohon ɗan Majalisar Wakilai Zakari Mohammed zai fafata a jihar Kwara.

A Plateau kuma, tsohon jami’in Sojojin Najeriya mai muƙamin Birgediya Janar, John Sunday Sura, ne zai tsaya takarar gwamna ƙarƙashin tutar ADC.

Jam’iyyar ta kuma gabatar da ’yan takara a Adamawa, Akwa Ibom, Borno, Cross River, Delta, Ebonyi, Enugu, Gombe, Jigawa, Kano, Katsina, Kebbi, Nasarawa, Niger, Ogun, Oyo, Rivers, Sokoto, Taraba, Yobe da Zamfara.

Kara karanta wannan

Ana batun zaben 2027, Kwankwaso ya aika sako kan makomar Najeriya

A jihar Lagos, Gbadebo Rhodes-Vivour zai tsaya takarar gwamna, yayin da Gbadamosi Babatunde Olalere zai kasance mataimakinsa.

A Kaduna kuwa, Isa Mohammed Ashiru zai yi takarar gwamna, tare da Kantiok Irmiya Ishaku a matsayin mataimakinsa, yayin da Ahmad Babba Kaita zai yi takara a Katsina.

Jerin ’yan takarar ADC da mataimakansu

1. Abia

Gwamna: Kalu Kalu Agu; Mataimaki: Alozie Ogadinma Darlington

2. Adamawa

Gwamna: Modibbo Hammantukur Ribadu; Mataimaki: Aguwa Kevin Iliya

3. Akwa Ibom

Gwamna: Akpanudoedehe John James; Mataimaki: Nsien Mkpombuk Tommy

4. Bauchi

Gwamna: Halliru Dauda Jika; Mataimaki: Sama’ila Mohammed Kabir

5. Benue

Gwamna: Herman Iorwase Hembe; Mataimaki: Abba John Abba

6. Borno

Gwamna: Babagana Buhari; Mataimaki: Mamman Dauda

7. Cross River

Gwamna: Nkoyo Toyo; Mataimaki: Okwocho Andrew Adagbor

8. Delta

Gwamna: Great Ogboru; Mataimaki: Afiari Gloria

9. Ebonyi

Gwamna: Ukpai Mba Udeh; Mataimaki: Onwe Daniel Ede

10. Enugu

Gwamna: Ocho Obodo Eze Chukwuma; Mataimaki: Eze Arinze Christopher

11. Gombe

Gwamna: Bala Bello; Mataimaki: Bala Sani Isa

12. Jigawa

Gwamna: Sabo Mohammed Nakudu; Mataimaki: Musa Ya’u Balarabe

Kara karanta wannan

2027: An samu matsala a taron hadakar jam'iyyun adawa domin kifar da Tinubu

13. Kaduna

Gwamna: Isa Mohammed Ashiru; Mataimaki: Kantiok Irmiya Ishaku

14. Kano

Gwamna: Ibrahim Ali Amin; Mataimaki: Shehu Abdulkadir Bari

15. Katsina

Gwamna: Ahmad Babba Kaita; Mataimaki: Aminu Yar’Adua Ahmed

16. Kebbi

Gwamna: Abubakar Malami; Mataimaki: Zagi Musa Mohammed

17. Kwara

Gwamna: Zakari Mohammed; Mataimaki: Olawuyi Julius Olayide

18. Legas

Gwamna: Gbadebo Rhodes-Vivour; Mataimaki: Gbadamosi Babatunde Olalere

19. Nasarawa

Gwamna: Nuhu Angbazo; Mataimaki: Ahmed Yusuf

20. Niger

Gwamna: Mohammed Kpautagi; Mataimaki: Musa Mamman

21. Ogun

Gwamna: Biodun Collins Ogundipe; Mataimaki: Muraina Oluwaranti Oluyemi

22. Oyo

Gwamna: Taofeek Adegboyega Adegoke Adegóke; Mataimaki: Wahab Adeniyi

23. Plateau

Gwamna: John Sunday Sura; Mataimaki: Pwa Jok-Kele Chundung Bitrus

24. Rivers

Gwamna: Gabriel Pidomson; Mataimaki: Okungba David Amapakaye

25. Sokoto

Gwamna: Manir Mohammad Daniya; Mataimaki: Isah Bello Ambarura

26. Taraba

Gwamna: Abubakar Umar Tutare; Mataimaki: Kwetishe Haruna Kwenyan

27. Yobe

Gwamna: Kassim G. Gaidam; Mataimaki: Kori Lawan Mohammed

28. Zamfara

Gwamna: Shinkafi Bilyaminu Yusuf; Mataimaki: Muhammad Abdulmuddalib Auwal

Kara karanta wannan

Mata ta kalli tawagar APC ido da ido, ta ce ko kuri'a 1 ba za su samu ba

ADC ta fitar da sunayen 'yan takarar gwamna
Dan takarar gwamnan ADC a Kaduna, Isa Ashiru Kudan Hoto: @IsaAshiruKudan
Source: Facebook

Dan takarar ADC zai ba dattawa alawus

A wani labarin kuma, kun ji cewa dan takarar gwamnan jam'iyyar ADC a Oyo, Olooye Adegboyega Taofeek Adegoke, ya yi alkawura ga dattawa.

Adegoke ya yi alkawarin biyan mazauna jihar ’yan shekara 75 zuwa sama alawus kowane wata.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal (Hausa Editor) Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng