
Manyan Labarai A Yau







Kungiyar kwadago (NLC) ta dakatar da shirinta na fara yajin aikin a fadin Najeriya a ranar Talata domin matsawa gwamnati kan ta magance wahalhalun mutane ke ciki.

Tsohon shugaban jam'iyyar All Progressives Congress na ƙasa, Sanata Abdullahi Adamu ya yi magana a karon farko tun bayan da ya yi murabus daga kujerarsa.

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya fara biyan ɗalibai mata na jihar Kano tallafin N20,000 duk wata domin taimaka musu wajen sauƙaƙa karatunsu.

A ranar Lahadi, 1 ga watan Oktoba, kamfanin BUA yasanar da karya farashin buhun siminti zuwa N3,500. Za a fara sayar da kaya kan sabon farashin daga ranar Litinin.

Wani mummunan hatsarin mota ya ritsa da mutane da dama akan titin hanyar Legas zuwa Ibadan. Mutum ɗaya ya rasa ransa yayin da wasu da dama suka raunata.

Gwamnatin tarayya a ranar Lahadi, 1 ga watan Oktoban 2023, ta sanar da ƙarin albashi da rabon tallafin kuɗi bayan ta kammala ganawa da ƙungiyar NLC.

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam'iyyar Labour Party (LP) a zaɓen 2023, Peter Obi, ya yi wa Shugaba Tinubu shaguɓe kan kan takardun bayanan karatunsa na jami'ar CSU.

Ministan Abuja, Nyesom Wike ya ce zanga-zangar ma’aikata kan tsige shugabannin hukumomi a Abuja baya damunsa domin dai abun da yake aikatawa shine daidai.

Shugaban kasa Tinubu ya amince da Karin albashin wucin gadi na N35,000 ga ma’aikata a dukkan mataki. Shugaban ma’aikatansa, Femi Gbajabiamila ne ya sanar da hakan.
Manyan Labarai A Yau
Samu kari