Manyan Labarai A Yau
Hukumar yaki da rashawa ta EFCC ta fara neman Sadiya Umar Farouq, wacce ta rike kujerar ministar jin kai karkashin gwamnatin Marigayi Muhammadu Buhari.
Magoya bayan Malam Nasir Ahmad El Rufai sun fara tara kudi da nufin saya masa fam din takarar shugaban kasa na jam'iyyar ADC, sun hada Naira miliyan 45.
Kwamitin tantancewa karkashin jagorancin shugaban jam'iyyar APC na kasa, Farfesa Nentawe Yilwatda ya fara tantance gwamnoni da sauran yan takara a Abuja.
Gwamnatin Turkiyya ta kaddamar da kazamin makami mai dogon zango da zai iya kaiwa zuwa nahiyoyin duniya. Yildirimhan zai iya kai wa mil 3,278 idan aka harba shi.
Sufeto Janar na rundunar yan sandan Najeriya, Olatunji Disu ya ba da umarnin gudanar da bincike kan zargin wasu jami'ai biyu da kisan Abubakar Idris Dadiyata.
Kamfanin sufurin jiragen sama na Rano Air ya dakatar da harkokinsa a wasu hanyoyi a Najeriya saboda tsadar farashin man jirgi, ya ce matakin na dan lokaci ne.
Tsohon shugaban kasa, Dr. Goodluck Ebele Jonathan ya bayyana cewa maganar bai halatta ya fito takara ba, batun ne da kotuna suka riga suka yi hukunci kansa.
Gwamnatin tarayya ta bayyana cewa ana yawan kuskure wajen ayyana sunan shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu da kujerar da yake kai, ta yi wa jama'a gyara.
Tsohon shugaban kasa a Botswana, Festus Mogae, ya yi bankwana da duniya. Marigayin ya mutu ne bayan ya kwashe lokaci yana jinya ta rashin lafiya.
Manyan Labarai A Yau
Samu kari