
Manyan Labarai A Yau







Majalisar wakilai ta fito ta yi magana kan zargin da aka jefe ta da shi na karbar cin hanci kafin amincewa da bukatar Shugaba Bola Tinubu kan dokar ta baci a Rivers.

Tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan ya yi magana kan matakin da Shugaba Bola Tinubu ya dauka na dakatar da Gwamna Siminalayi Fubara na Rivers.

Wasu miyagun 'yan bindiga dauke da makamai sun kai harin ta'addanci a babban birnin tarayya Abuja. 'Yan bindigan sun yi awon gaba da wata soja da wasu mutum biyu.

Dan majalisar wakilai daga jihar Jigawa, Yusuf Shittu Galambi, ya musanta zargin da ake jifan 'yan majalisa da shi na karbar cin hanci kan dokar ta baci a Rivers.

Dakarun sojoji sun yi gumurzu da 'yan ta'addan Lakurawa a jihar Kebbi. Jami'an tsaron sun samu nasarar hallaka 'yan ta'addan kungiyar tare da kwato masu yawa.

Kungiyar shugabannin kananan hukumomi ta Najeriya (ALGON), ta tabo batun da ya sanya har yanzu gwamnatin tarayya ba ta fara tura musu kudade kai tsaye ba.

Kungiyar dattawan Arewa ta yi fatali da dakatar da Gwamna Fubara, mataimakiyarsa da ƴan Majalisar Dokoki, ta ce hakan ya saɓawa tanadin dokar ƙasa.

Alhaji Nasiru Ahali, attajiri kuma ɗaya daga cikin shuwagabannin masana’antu na farko a Kano, ya rasu yana da shekaru 108, inda za a yi jana’izarsa a Kurna Asabe.

Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan ta ce ta kwashe fiye da shekara guda tana fama da yunkurin cin zarafi daga shugaban majalisar dattawa, Godswill Akpabio.
Manyan Labarai A Yau
Samu kari