Shugabannin Kwamitin Yakin Zabe da aka yi kafin Abdulaziz Yari daga 1999 zuwa 2027
FCT, Abuja - Fadar shugaban kasa ta nada Abdulaziz Yari ya zama shugaban yakin neman zaben Bola Tinubu/Kashim Shettima
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
M Malumfashi ya shafe shekaru 10 yana kawo labaran Hausa musamman na siyasa, addini, tarihi, wasanni da al’ada
Kafin Sanata Abdulaziz Yari, an samu wasu ‘yan siyasa da suka rike matsayin Darekta Janar na yakin zaben shugaban kasa a kasar nan.
A rahoton nan, mun tattaro shugabannin kamfe da suka kai jam’yyun PDP da APC ga nasara a takarar shugaban kasa tun daga 1999.

Source: Getty Images
Tarihin darektoci janar na kame daga 1999
Shugabannin kamfe da suka ci zabe bayan dawo wa mulkin farar hula sun kunshi Iyorchia Ayu, Adamu Ciroma da irinsu Bode George.
Baya ga ‘yan PDP, an samu Rotimi Amaechi da Sanata Simon Lalong a jam’iyyar APC.
PDP ta rika cinye kimanin 60% na kuri’u a zabukan 1999 zuwa na 2015, sai dai adadin ya ragu lokacin takarar Muhammadu Buhari.
Da Bola Tinubu ya nemi mulki a shekarar 2023 kuwa, 36.6% na kuri’un da aka kada ya samu.
Iyorchia Ayu, Fidelis Tapgun, Rotimi Amaechi, Simon Lalong duk sun zama ministoci bayan an kafa gwamntocin tarayya da aka lashe zabe.
Shugabannin kwamitin yakin zaben shugaban kasa
1. Iyorchia Ayu
Sanata Iyorchia Ayu shi ne ya jagoranci yakin neman zaben Olusegun Obasanjo lokacin da ya nemi mulkin Najeriya a 1999 a karkashin PDP.
A wata hira da Vanguard, ‘dan siyasar ya ce Atiku ya hada shi da Obasanjo. Sai dai bai iya rike wannan matsayi da aka zo zaben 2003 ba.
2. Fidelis Tapgun
Da Obasanjo yake so ya zarce, sai ya dauko tsohon gwamna Fidelis Tapgun ya zama Darekta Janar na kamfe, da ya ci zabe ya nada shi minista.
A lokacin Adamu Ciroma ya taka rawar gani wajen yakin neman babban zabe. Tsohon gwamnan na CBN ya yi Ministan kudi a zamanin na PDP.
3. Bode George
Bode George ne shugaban yakin neman zaben Ummaru Musa Yar’adua da Goodluck Jonathan a zaben 2007, kuma PDP ta samu nasara a takarar.

Kara karanta wannan
Ko Tinubu na da abubuwan da zai shawo kan 'yan Najeriya su zaɓi APC a 2027? An samu bayani
Tsohon gwamnan na mulkin soja ya taka rawar gani, sai dai har gobe ana sukar zaben na 2007 da cewa an shirya gagarumar magudi a Najeriya.
4. Ahmadu Ali
Ahmadu Ali wanda ya taba zama minista da sanata ya jagoranci tallata Goodluck Jonathan a 2011 har PDP ta doke CPC, ACN da ANPP.
Ali ya yi wannan aiki tare da Dalhatu Sarki Tafida, Jonathan ya samu 58.9% na kuri’u duk da nasarar da Muhammadu Buhari y samu a Arewa.

Source: Getty Images
5. Rotimi Amaechi
Rotimi Amaechi ne Darekta Janar a zaben 2015 da ya kawo karshen mulkin PDP, shi ya jagoranci kamfen Muhammadu Buhari a jam’iyyar APC.
Ko da za a shiga zaben 2023, shi ya sake zama shugaban yakin zabe. A gwamnatin APC ya yi kusan shekaru takwas yana Babban Ministan sufuri.
6. Simon Lalong
Shi Bola Tinubu ya dauko Simon Lalong - kirista daga Filato ya zama shugaban yakin neman zabensa lokacin da ya duako danuwansa musulmi.
APC ta ci zaben 2023 amma kamar yadda Rotimi Amaechi bai iya ba jam'iyyarsa nasara a Ribas ba, shi ma tsohon gwamnan ya ji kunya a jihar Filato.
Babu wasu manya a kwamitin kamfen APC
Wannan labari ya yi duba ne kan jerin manyan 'yan siyasa na APC kamar Nuhu Ribadu, Dikko Radda, da Abba Kabir Yusuf da ba su cikin kamfe.
Rahoton ya zakulo jami'ai da 'yan siyasa daban-daban da aka bar su a waje duk da irin gudunmuwar da suka bayar ko kuma matsayinsu na siyasa a kasa.
Gwamnoni masu-ci, tsofaffi da shugabannin majalisa da na yanzu da jagorori a APC suna cikin wadanda babu su a kwamitin kamfen Tinubu/Shettima.
Asali: Legit.ng

