Kwankwaso Ya Yi Magana kan Kwamitin Kamfen din Tinubu, Ya Aika Sako ga Sanata Yari
- Rabiu Kwankwaso ya soki tsarin kwamitin yakin neman zaɓen APC na 2027, yana mai tambayar irin abin da jam’iyyar ke son gabatar wa ’yan Najeriya
- Ɗan takarar mataimakin shugaban ƙasa na NDC ya buƙaci Abdul’aziz Yari ya sake duba matsayinsa na jagorantar kamfen din Tinubu
- Kwankwaso ya kuma nuna damuwa kan rawar da manyan jami’an gwamnati ke takawa a tsarin tara kuɗaɗen kamfen
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi
FCT, Abuja - Mataimakin ɗan takarar shugaban ƙasa na NDC, Rabiu Musa Kwankwaso, ya soki tsarin kwamitin yakin neman zaɓen APC na zaɓen 2027.
Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya kuma buƙaci Abdul’aziz Yari ya sake duba matsayinsa na jagorantar yakin neman zaben Shugaba Tinubu a 2027.

Source: Facebook
Kwankwaso ya bayyana hakan ne a wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na X ranar Lahadi, 23 ga watan Agustan 2026.
Madugun na Kwankwasiyya ya tambayi dalilin da ya sa Yari, tsohon gwamnan jihar Zamfara kuma jigo a APC, ya amince ya jagoranci kamfen ɗin sake zaɓen Shugaba Bola Tinubu.
Kwankwaso ya soki tsarin kamfen din Tinubu
A cewar Kwankwaso, tsarin kwamitin ya nuna cewa jam’iyyar mai mulki tana dogaro da ’yan siyasar da suka goyi bayan gwamnatin yanzu ko kuma suka taɓa kasancewa a cikinta.
Ya ce hakan na haifar da tambayar abin da APC ke shirin gabatar wa masu zaɓe a shekarar 2027.
“Kwamitin ya haɗa da da yawa daga cikin ’yan siyasar da suka goyi bayan gwamnatin yanzu, suka kare ta ko kuma suka shiga cikinta."
“Haɗuwarsu ta haifar da wata muhimmiyar tambaya: me suke son ’yan Najeriya su zaɓa a 2027, sabon farawa ne ko kuma ci gaba da tsarin da ya jefa al’ummarmu cikin tsananin wahala?” in ji shi.
Kwankwaso ya ce zaɓen shugaban ƙasa na 2027 zai bai wa ’yan Najeriya damar yanke shawarar ko za su ci gaba da riƙe da gwamnatin yanzu ko kuma su nemi wata hanya dabam.

Kara karanta wannan
Ba tare da tsoro ba, Kwankwaso ya fadi rukunin mutane 2 da za su gwabza a zaben 2027
Ya lissafa tsadar rayuwa, rashin aikin yi, rashin tsaro da matsin lamba kan ilimi, kiwon lafiya da sauran ayyukan gwamnati a matsayin wasu daga cikin ƙalubalen da ’yan Najeriya ke fuskanta.
Kwankwaso ya nemi Yari ya sake tunani
Tsohon gwamnan na Kano ya yi kira na musamman ga Yari da ya sake duba shawarar da ya yanke ta jagorantar kamfen ɗin Tinubu.
Kwankwaso ya ce kwarewar Yari a matsayin tsohon gwamnan Zamfara ya kamata ta sa ya fahimci matsalolin da ’yan Najeriya ke fuskanta, musamman a yankin Arewa maso Yamma.
“A matsayinsa na tsohon gwamnan jihar Zamfara kuma fitaccen jagora daga Arewa maso Yamma, na yi amanna cewa Sanata Yari ya fahimci illolin rashin tsaro, talauci, rashin aikin yi, ƙaura da lalacewar hanyoyin samun abin rayuwa a yankin da ma ƙasar baki ɗaya,” in ji shi.
Kwankwaso ya tambayi ko Yari zai ji daɗin jagorantar kamfen ɗin neman wa gwamnatin Tinubu wa’adi na biyu, alhali kuwa yana fuskantar matsalolin da ya ce ’yan Najeriya ke fama da su.

Source: Facebook
Ya yi magana kan jami’an gwamnati
Kwankwaso ya kuma nuna damuwa kan rahotannin da suka ce an saka Shugaban Hukumar Kula da Haraji ta Najeriya, Zacch Adedeji, da Darakta-Janar na Ofishin Kasafin Kuɗi na Tarayya, Tanimu Yakubu Kurfi, cikin tsarin tara kuɗaɗe da harkokin kuɗin kamfen.
A cewarsa, shigar manyan jami’an gwamnati cikin ayyukan kamfen na jam’iyya na haifar da tambayoyi kan tsaka-tsakin hukumomin gwamnati da kuma amincewar jama’a.
Kwankwaso ya yi kira ga 'yan Najeriya
Kwankwaso ya kuma yi kira ga ’yan Najeriya da su ƙi abin da ya bayyana a matsayin ci gaba da danniya, tare da zaɓar shugabanci mai riƙon amana da kuma mai fifita bukatun jama’a a 2027.
“Idan mutanen Osun sun iya yin hakan, sauran sassan ƙasar ma za su iya,” in ji shi.
Tinubu zai kayar da Kwankwaso a Kano
A wani labarin kuma, kun ji cewa dan majalisar wakilai, Abdulmumin jibrin, ya nuna kwarin gwiwar cewa Shugaba Bola Tinubu zai kayar da Sanata Rabiu Musa Kwankwaso a Kano a zaben 2027.
Dan majalisar ya nuna cewa Tinubu zai kayar da tsohon gwamnan ne saboda ba shi ba ne dan takarar shugaban kasa na jam'iyyar NDC.
Asali: Legit.ng

