Gwamna Abba Ya Rabawa Hadimai Filaye da Kudi, Ya Yi Magana kan Zaben Tinubu a 2027

Gwamna Abba Ya Rabawa Hadimai Filaye da Kudi, Ya Yi Magana kan Zaben Tinubu a 2027

  • Gwamna jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya jaddada goyon bayansa ga tazarcen shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu a zaben 2027
  • Abba Gida Gida ya bayyana cewa jam'iyyar APC reshen jihar Kano za ta yi duk mai yiwuwa wajen tabbatar da nassra a kowane mataki
  • ya ce Kano za ta yi aiki domin APC ta yi nasara a zaɓen 2027
  • Gwamnan ya ce sake zaɓen Shugaba Tinubu da yi masa kamfe a lungu da sako nauyi ne da ya rataya a wuyan dukkan mambobin jam'iyyar

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Kano, Nigeria - Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya bayyana cewa gwamnatinsa za ta yi duk mai yiwuwa domin tabbatar da nasarar APC zaɓen 2027.

Ya kuma buƙaci duk masu riƙe da muƙaman siyasa a gwamnatinsa su shiga sahun masu yaɗa jam'iyyar tare da ƙarfafa shirinta a faɗin jihar.

Kara karanta wannan

Akwai matsala: Har yanzu ba a bai wa hukumar INEC kuɗin shirya babban zaben 2027 ba

Gwamna Abba.
Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf yana jawabi a taron rabawa magoya bayansa babura a gidan gwamnati Hoto: Sanusi Bature D-Tofa
Source: Facebook

Daily Trust ta rahoto cewa Abba ya bayyana hakan ne yayin wani taron tattaunawa da aka gudanar da zaɓaɓɓun shugabanni da masu muƙaman gwamnati a gidan gwamnatin Kano.

Gwamnatin Kano na tare da Tinubu

A cewar sanarwar da mai magana da yawunsa, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya fitar, Abba Kabir ya ce Kano za ta kasance kan gaba wajen tabbatar da Tinubu ya samu ƙuri'u masu yawa a zaɓen shugaban ƙasa na 2027.

Ya ce gwamnatinsa ba ta da wata nadama kan goyon bayan Tinubu, yana mai cewa sake zaɓensa nauyi ne da ya rataya a wuyan dukkan jami'an gwamnati da mambobin APC.

Gwamnan ya umarci duk masu muƙaman siyasa da har yanzu ba su yi rajista a APC ba da su gaggauta yin hakan, yana mai cewa dole ne kowane zaɓaɓɓe ko naɗaɗɗen jami'i ya kasance cikakken ɗan jam'iyyar.

Abba ya rabawa hadimansa filaye

Kara karanta wannan

Da gaske tsohon gwamna ya mutu a Najeriya? Gwamnatin Delta ta tsage gaskiya

Domin ƙarfafa gwiwar masu riƙe da muƙaman siyasa, Gwamna Yusuf ya amince da rabon filaye ga hadimansa sama da 300.

Waɗanda za su amfana sun haɗa da manyan mataimaka na musamman (SSA), mataimaka na musamman (SA), manyan masu dauko rahoto na musamman, masu dauko rahoto na musamman da mataimaka na kai da kai

Haka kuma Abba Gida-Gida ya amince a bai wa kowanne daga cikin wadannan hadimai da aka ambata kyautar N100,000.

Abba da Tinubu.
Gwamna Abba Kabir Yusuf tare da Shugaba Bola Ahmed Tinubu lokacin da ya kai masa ziyara a Aso Rock Hoto: @aonanuga1956
Source: Twitter

APC ta ce ta shirya tunkarar 2027

Da yake jawabi a taron, Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kano, Rt. Hon. Ismail Falgore, ya ce APC za ta ci gaba da tallata ayyukan da Shugaba Tinubu ya gudanar domin ƙara samun karɓuwa a jihar.

Shi ma shugaban APC na jihar Kano, Hon. Umar Haruna Doguwa, ya bayyana cewa jam'iyyar ta shirya tsaf domin zaɓen 2027.

Abba ya yi garambawul a gwamnati

A baya, kun ji cewa Gwamna Abba Kabir Yusuf ya yi sauye-sauyen masu ba shi shawara.domin inganta aiki a gwamnatin jihar Kano.

Haka kuma gwamnan ya amince da waɗansu sababbin nade-naden domin karfafa tsarin mulki da inganta ayyukan gwamnati.

Abba Kabir ya amince da nada Bello Nuhu Bello a matsayin mai ba da shawara kan harkokin gudanarwa a ofishin gwamna.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262