Shugaba Tinubu Ya Maida Hankali kan Samar da Ayyuka Masu Gwabi ga Matasan Najeriya
- Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ya maida hankali kan fadada damar samun ilimi da horo ga matasa yan Najeriya
- Hadimin shugaban kasa kan harkokin dalibai, Kwamared Sunday Asfon ne ya bayyana hakan a bikin ranar matasa ta duniya
- Ya bukaci matasa su rungumi sababbin dabaru, zaman lafiya da taimakon juna domin dogaro da kansu
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Abuja, Nigeria - Babban Mataimaki na Musamman ga Shugaban Kasa kan Harkokin Dalibai, Kwamred Sunday Asefon, ya sake jaddada kudirin Shugaba Bola Ahmed Tinubu na sama wa matasa ayyukan yi.
Ya ce Shugaba Tinubu ya maida hankali wajen fadada damar samun ilimi, bunkasa kirkire-kirkire da samar da damarmakin aiki masu kyau ga matasan Najeriya.

Source: Twitter
Tribune Nigeria ta rahoto cewa Asefon ya bayyana hakan ne ranar Laraba a sakonsa ga matasan Najeriya domin tunawa da ranar matasa ta duniya ta 2026.
Matasan Najeriya na da buri iri daya
Ya ce taken ranar matasa ta bana ya nuna irin burin da matasa ke da shi duk da bambancin yanayinsu da wuraren da suke rayuwa.
Ya ce daga cikin wadannan buri akwai samun ingantaccen ilimi, aikin yi mai kyau, kirkire-kirkire, hada kai, tsaro da kuma damar amfani da baiwa wajen samar da tasiri mai amfani ga al’umma.
A cewarsa, hulda da dalibai da matasa a jami’o’i da sauran cibiyoyin ilimi ta kara tabbatar masa da cewa bai kamata a rika kallon matasan Najeriya a matsayin “shugabannin gobe” kawai ba.
Ya ce ya kamata a dauke su a matsayin abokan hadin gwiwa wajen gina Najeriya ta yau da kuma makomar kasar.
Gwamnatin Tinubu na tallafa wa matasa
Asefon ya ce gwamnatin Tinubu ta kuduri aniyar samar da yanayin da zai bai wa matasan Najeriya damar samun kwarewar da ake bukata, samun ilimi, cin gajiyar damarmakin zamani da kuma bunkasa harkokin kasuwanci.
Ya ce gwamnati na aiwatar da shirye-shirye a fannonin ilimi, bunkasa kwarewa, amfani da fasahar zamani, tallafa wa dalibai, kasuwanci da kirkire-kirkire domin tabbatar da cewa babu wani matashi da aka bari a baya.
Ya ce:
“Bambancin yanayin da muke ciki bai kamata ya zama katanga ga burinmu na bai daya ba. Ko matashi yana Legas ko Lafia, Enugu ko Ekiti, Kano ko Calabar, burinmu yana hade da sha’awar ganin Najeriya ta zama kasa mafi kyau.”

Source: Facebook
Ya bukaci matasa su tashi tsaye
Hadimin shugaban kasar ya bukaci matasan Najeriya da su daina kallon kansu a matsayin masu cin gajiyar shirye-shiryen gwamnati kawai, su rungumi rawar da za su taka wajen samar da irin Najeriya da suke muradi.
Ya bukaci matasa su rungumi kirkire-kirkire, su koyi sabbin dabaru, su inganta zaman lafiya, su yi watsi da tashin hankali tare da taimakon juna.
Gwamnati za ta samar da ayyuka 50,000
A wani labarin, kun ji cewa gwamnatin tarayya ta ƙaddamar da Tinubu Light Initiative (TLI ) , wani shiri na samar da makamashin lantarki mai tsafta a faɗin ƙasa.
na sa ran wannan shiri zai samar da ayyukan yi kai tsayelsama da 50,000, ga matsa yan Najeriya tare da rage farashin gudanar da kasuwanci.
Asali: Legit.ng

